Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa
Published: February 27, 2026 at 4:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Akwai manyan batutuwa ko rashin fahimta dake kunno kai a yarjejeniyar kiwon lafiya da Amurka take kullawa da kasashen Afirka dangane da yadda tallafin kudi da Amurka take bayarwa zai rika aiki daga yanzu, kamar yadda shugaban hukumar sa ido da hana yaduwar cututtuka a Afirka ya fada ranar Alhamis.

“Akwai damuwa sosai game da musayar bayanai dana cututtuka, inji darekta janar na hukumar Jean Kesaya ya fadawa taron manema labarai ta hanyoyin sadarwa na zamani.

Ranar Laraba, Zimbabwe ta janye daga shawarwari da Amurka kan tallafin kudi dala milyan 367 cikin shekaru biyar masu zuwa, ta nuna damuwa kan musayar muhimman bayanai, tana mai cewa yarjejeniyar babu adalci. Zambia ma tace ta nuna rashin gamsuwarta da tsarin.

Wasu masu raji kan kiwon lafiya sun soki tsari da ya bukaci kasashe ba-da-wani-bata-lokaci ba, su sanarda Washington idan aka sami bullar wata cuta mai yaduwa a zaman sharadin bada tallafin. Yarjejeniyoyin basu bada tabbacin idan aka hada maganin da zai shawo kan cuta ko cututtukan za’a raba da kasashen da cutuutkan suka bullo ba.

Ahalinda ake ciki kuma, a cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da Amurka da jamhuriyar demokuradiyyar kwango suka sanyawa hanu ranar Alhamis, ta nuna kasashen biyu sun amince da yarjejeniyar aiki ta fuskar kiwon lafiya kan kudi dala bilyan daya da milyan dari biyu, cikin shekaru biyar masu zuwa.

Yarjejeniyar zata maida hankali kan yaki da cutar dake karya garkuwar jiki, da ake yi wa lakabin HIV/AIDS da turanci, da cutar Malaria, da kuma kula da lafiyar iyaye mata masu juna biyu da jarirai, yaki da cutar shan inno ko polio, da kuma sa ido kan pullar cututtuka masu yaduwa, kamar yadda sanarwar ta fada.

Afrika, Amurka, Kimiya, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC
Next Post: Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo Labarai
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.