Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar
Published: February 28, 2026 at 3:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa an sace yara 48 ‘yan asalin jihar masu shekaru tsakanin biyu zuwa biyar, inda ya ce an kai su wasu sassan duniya kamar yadda jaridar The Cable ta rawaito.

Inuwa Yahaya ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da rabon tallafin Abincin Ramadan a Gombe, inda ya nuna damuwa kan rashin tabbacin ko za a sake samun yaran lafiya.

Yace tsaro alhakin kowa ne, tare da buƙatar mazauna jihar su mara wa matakan gwamnati baya domin dakile barazanar da ke addabar zaman lafiya.

Gwamnan ya kuma ce dokar hana cinikin ƙarafa da takaita amfani da babura an ɗauke su ne domin inganta tsaro da rage satar ababen hawa.

Haka zalika, ya koka kan lalata kayayyakin more rayuwa, inda ya ce an taɓa kayayyakin wutar lantarki na Muhammadu Buhari Industrial Park da kuma madatsar ruwa ta Dadin Kowa Dam.

Ya ƙara da cewa mutane 70,000 ne za su amfana da tallafin Ramadan, tare da umartar kwamitin rabon kayayyakin da su tabbatar da gaskiya da adalci kuma Suyi rabon a cikin mako daya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu
Next Post: Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
Tarkacen Makamai Masu Linzami Sun Lalata Gidaje Da Wuraren Kasuwancin Palasdinawa Afrika
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.