A ci gaba da tallafawa wa al’umar musulmai a fadin duniya don su samu saukin rayuwa musamman wannan lokaci na watan Ramadan wata mai alfarma watan da ake neman falalar Ubangiji.
Alh Al’mustapha Haji Sufi Hasken Matasan Arewa da ke jihar Bauchi Arewa maso gabas a Najeriya ya taimaka wa Zawiya da Marayu da kuma marasa galihu da abunda zasu samu su ci a lokacin boda baki.
Sama da Zawiya 100 ne suka amfana da Shinkafa, Taliya Mangya, da dai sauran kayayyaki da kuma kudade a ka raba a wajan.
An raba shinkafa mai nauyin kilogram 50 da kuma kilogram 25, guda 200, da kuma mangyada Katon Tamanin da Katon din Taliya 100 tare da kimanin kudi sama da miliyon daya ne aka raba a wajan.
A yayin jawabinsa Al’mustapha yace Al’mustapha Haji Sufi yace wannan gudumawa ya fito ne ta hannuna hukumar raya Arewa maso gabas NEDC ta re da Kwamishinan Kudi na Jihar Bauchi Hon Yakubu Adamu PhD.

babban dalilinsa na irin wannan taimako shine ganin irin halin da al’umma suke cikin halin mawuyacin rayuwa a yanzu haka, kuma ni Mutumne da aduk lokacin da na samu alheri daga wani waje na kanso ace nima na taimaka wa na kasa dani dai dai gwargwadon abunda zan iya kuma gashi lokacin wata mai Albarka na Ramadan.’
Babban bako a wajan Alh Nasiru Musa Sudani ya yaba da kokari irin wadda Alh Al’mustapha Haji Sufi Hasken Matasan Arewa inda yace ba wannane na farko da ya fara ba sama da shekaru goma yana yin aikin alheri wa al’uma.”

Yace saboda irin wannan abun alheri da Al’mustapha ya ke shi yasaea kulllum al’uma ki masa fatan alheri a rayuwar sa, ya kuma masa fatan alheri a dukkanin rayuwar sa.
Cikin wayanda suka samu wannan tallafi harda masu bukata ta musamman da kuma al’umar da suke gidan gyara hali da tarbiya na Bauchi.

Wasu daga cikin wayanda suka amfana da wannan tallafi sukace zasuyi amfani da wannan tallafi wajan Shan Ruwa a wannan wata mai alfarma kuma zasu sanya shi cikin addu’oin su a wannan watan Ramadan.


