Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo
Published: November 25, 2025 at 2:12 PM | By: Bala Hassan | Updated: November 25, 2025

Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist

Tabbas Wikki Tourist ta samu shuwagabanin da zasu cire mata kitse a wuta. Wannan yabo ya fito ne ta bakin Shugaban ƙungiyar Magoya bayan Ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist Fc da ke Bauchi a tarayyar Najeriya. Alh Umar (Aljan) yayi karin hasake a wata ganawa da yayi da wakilin GTA Hausa.

Umar ya ce ƙungiyar ta samu dai dai tuwa a karkashin jagorancin shugaban gudanawar Kulub din Alh. Auwal Gotel, lura da yadda ƙungiyar ta ke samun nasara a wasannin ta a gida da waje ” In ji Aljan.

Yace a baya akwai wasu abubuwa na kurakurai da aka yi bangaren Shuwagabanni sakamakon jan hankali da ake musu ta kafafen yada labari ko mai ya dai dai ta a yanzu.

Har ila yau ‘Aljan, ya yaba wa manbobinsa bangaren magoya baya bisa yadda suke bin doka da oda wajan ganin anyi wasa lafiya, don kuwa ko da za’a zo gida a Wikki Tourist ta yi kunnen doki baza a ta da yamutsi ba, kamar yadda wasu ƙungiyoyin ke yi.

A ranar Lahadi da ta gabata ƙungiyar kwallon kafa ta Bayelsa United ta zo har gida ta rike Wikki 1-1 a wasan mako na 14, cikin gasar Firimiyar Najeriya na bana, amman babu wani abun da ya faru na cin mutuncin alkalin wasa ko wani jami’i, duk da irin kurakuren da baza’a rasa ba daga Alkalin wasa.

Umar yace duk kulub din Arewa da suke buga gasar Firimiyar Najeriya NPFL 2025/26 babu wadda ta kai Wikki Tourist kokari ganin yadda ita ce kawai ba’ayi nasara akanta a gidan ta ba.

Yanzu haka Wikki Tourist FC ta na mataki na 7 a teburen gasar Firimiyar Najeriya mako na 14, a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamban 2025, zata kai bakunci zuwa gidan ƙungiyar kwallon kafa ta Bendel Insurance FC, wasannin mako na 15.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City
Next Post: An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF Wasanni
Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
Al Hilal Ta Cimma Yarjejeniya Da Pedro Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
  • Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.