Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
Published: March 17, 2026 at 9:28 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhininsa game da sabon harin ta’addanci da aka kai birnin Maiduguri na jihar Borno, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin bacin rai da ban takaici.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, 17 ga watan Maris, 2026, Shugaba Tinubu ya jajantawa mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, yana mai jaddada cewa gwamnati na tare da jama’ar Jihar Borno a wannan mawuyacin lokaci.

Shugaban ya bayyana cewa wadannan hare-hare na nuna alamun fargaba da matsin lamba da ’yan ta’addan ke fuskanta daga dakarun tsaron Najeriya.
“Wadannan ayyukan ta’addanci yunƙuri ne na ƙarshe na matsananciyar fargaba da waɗannan masu laifin ke yi domin dasa tsoro a zukatan mutane, sakamakon irin luguden wutar da suke fuskanta daga jami’anmu.” Inji Tinubu

Tinubu ya ƙara da cewa, a taron tsaro da ya gudanar a ƙarshen makon jiya, ya amince da samar da ƙarin kayan aiki da tallafin ayyuka ga hukumomin tsaro domin ƙarfafa dabarunsu na yaƙi da ta’addanci.

Domin tabbatar da an magance lamarin cikin gaggawa, Shugaba Tinubu ya ba wa manyan hafsoshin tsaro na ƙasa umarnin gaggawa na su koma birnin Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro da kansu.

Haka kuma, ya umarci hukumomin agajin gaggawa da su tabbatar da sun ba wa duk waɗanda suka jikkata kulawar da ta dace.

A ƙarshe, Shugaban ya jaddada cewa babu wani lungu a Najeriya da zai zama wurin buya ga ’yan ta’adda, inda ya ce, “Ba za mu taba mika wuya ga tsoro ba. Za mu nemo su, mu fuskance su, kuma mu murƙushe su baki ɗaya.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
Next Post: Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu Najeriya
Yayale Ahmed Ya Jagoranci Kwamitin Amintattu Na Asusun Tsaron Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kaduna: Masana Sun Nemi A Sauya Tsohon Wurin Zubar Da Shara Na Tudun-Ilu Afrika
  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki Afrika
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.