Hare-haren da jiragen yaki marasa matuka suka kai birnin Goma da ke gabashin Kongo a ranar Laraba, inda suka kashe akalla mutane uku ciki har da wani ma’aikacin agaji dan kasar Faransa, wanda shi ne hari na farko da aka kai a birnin tun bayan da ‘yan tawayen AFC/M23 suka kwace birnin a bara, a cewar kungiyar da kuma MDD.
Kungiyar ta AFC/M23 ta dora alhakin harin kan sojojin Kongo, inda ta ce a wani sakon da ta wallafa a shafinta na X cewa Kinshasa ta harba jirage masu saukar ungulu a wani yanki mai yawan jama’a a birnin da ke gefen tafkin.
Wani mai magana da yawun ‘yan tawayen ya fada a wani sako na daban cewa mutane uku sun mutu, ciki har da wani ma’aikacin jin kai na kasashen waje.
Wani babban jami’in hukumar kula da yara ta Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an kashe daya daga cikin ma’aikatanta, dan kasar Faransa.
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a Kongo ta tabbatar da cewa harin ya kashe wani ma’aikacin Majalisar Dinkin Duniya da wasu fararen hula biyu tare da gargadin cewa hare-haren da ake kaiwa jami’an Majalisar Dinkin Duniya na iya zama laifukan yaki.


