An tsinto gawarwakin mutane 17 a cikin wani kwalekwale dauke da ‘yan gudun hijira a bakin tekun Comoros, a cewar ministan cikin gida na tsibirin dake tekun India Mohamed Ahamada.
Hukumomi sun ce suna ganin ‘yan gudun hijiran na kokarin isa Mayotte, yankin rainon Faransa dake tsakanin Mozambique da Madagascar.
Mohamed Ahmada yace mutanen 30 sun tsira da rayukan su a jirgin.
A yayin da caca ta yanar gizo take kara samun wurin zama a nahiyar Afirka, gwamnatoci na kara kudin harajin caca domin shawo kan abun, da kuma bunkasa asusun kasa. A kasar Afirka ta Kudu, wadda ita ce kan gaba wajen wadanda suka fi yin cacar, masu sana’ar na sukan matakin da gwamnatocin suka dauka.


