Kasar Kenya ranar Litinin tace tana samun karin fasinjoji a jiragen ta na Kenyan Airways sakamakon yakin Gabas ta Tsakiya, inda yawanci fasinjojin daga Turai ne Asia da Amurka.
Yakin da Amurka da Isra’ila suke yi da Iran ya hargitsa zirga-zirgar jiragen sama na duniya, abinda ya jawo wasu kamfanonin jiragen kara kudi da kuma sauya hanyoyin da suke bi don kaucewa yawan tsayawa a filayen jirgin sama na Gabas ta Tsakiya, koma su soke tafiyar gaba daya.
Kamfanin Kenyan Airways yace yanzu masu son shiga jiragen su sun kai kusan kashi 100 cikin 100, wanda da a baya a watan Janairu kashi 70 cikin 100 ne kawai.


