Kungiyar mayakan Houthi a Yemen mai samun goyon bayan Iran ta fada jiya jumma’a cewa, a shirye take ta fada yakin hadin guiwar da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan Iran idan wasu kasashe suka shiga yakin a gefen Amurka da Isra’ila, ko kuma idan aka yi amfani da bahar maliya wajen kaddamar da hari kan jamhuriyar Farisan mai bin tafarkin Islama, kamar yadda kakakin kungiyar mayakan sakan Yahya Saree, ya fada ta gidan talabijin.
Saree, yace a shirye kungiyar take ta shiga yakin, muddin aka ci gaba da zafafa hare hare kan Iran da kuma wadanda ya kira “murhun kare kai,” sai dai bai fayyace ta irin yadda za su shiga yakin da ake yi ba.
Gargadin da kungiyar ta Houthi tayi, yana kara nuna yadda yakin zai iya ba zuwa ya shafi yankin duka, musamman ganin karfin kungiyar na kai farmaki nesa daga Yemen, da kuma kassara zirga zirga a ruwayen da suke yankin na zirin Arabaiya.
Tuni kawayen Iran ‘yan shi’a a Lebanon da Iraqi suka shiga yakin da ake yi a yankin, sakamakon harin da Amurka da Isra’ila suka auna kan Iran.


