A yayinda ake ci gaba da jimami da kuma neman yadda za’a samu kubutar da sauran Daliban Makarantar St. Mary a jihar Nejan Najeriya da ‘yan bindiga suka kwashe a Makon jiya.
Yanzu haka kuma wasu ‘yan fashin Dajin sun kai wani sabon hari a yankin Shiroro tare da yin awon gaba da wasu Mutane.
Dama dai yankin na Shiroro mai madatsar ruwan dake da daya daga cikin tashoshin dake samar da hasken lantarki a Najeriya ya dade yana fama da matsalar hare haren ‘yan bindigar.
Wani mazaunin yankin karamar Hukumar Shiroron da ya bukaci a sakaya sunanshi yace maharan sun shiga kauyen Unguwar kawo ne a ranar Laraban nan su kayi awon gaba da mutane takwas, uku daga cikinsu mata ne da kuma karamin yaro guda.
Rundunar ‘yansanda ta Jihar Nejan ta tabbatar da aukuwar lamarin sai dai tace bata gama tantance abinda ya faruba, kakakin yandan Wasiu Abiodun yace ya zuwa lokacin da muka tuntube shi basu fayyace abinda ya faruba.
Yace yaji batun harin amma zai kara bincikawa domin ba zai iya baka ainahin yawan mutanen da aka sacenba.
Bincike dai ya nuna a yanzu haka akwai garuruwa da dama a yankin Arewacin Jihar Nejan da kuma Arewa maso gabas da suka koma kufai saboda ‘yanbindigar sun fatattaki jama’a daga garuruwan.


