Wani rahoto daga hukumomi biyu na Majalisar Dinkin Duniya, Kungiyar Tarayyar Afirka da Bankin Raya Tattalin Arzikin Afirka (ADB) suka saki a ranar Alhamis, yace ci gaban tattalin arzikin kasashen Afrika zai fuskanci jinkiri sosai a wannan shekarar idan aka ci gaba da yakin Gabas ta tsakiya, tare da kawo hargitsi a cinikayya na lokaci mai tsawo, da samar da makamashi da taki a duk fadin nahiyar.
Rahoton yace kasashen Afirka zasu iya yin asarar kashi 0.2 cikin 100 na tattalin arzikin su a shekarar 2026 idan yakin ya zarce wata 6.
Rahoton bai yi bayani kan yadda abun zai shafi hauhawar farashi ba, amma yayi gargadin cewa yakin nan da nan zai iya haddasa rikicin tsadar rayuwa ta hanyar karuwar farashin mai da abinci. Yace wasu kasashen Afirka zasu fi fuskantar rashin isasshen takin zamani, bisa ga hauhawar farashin mai.


