Fargaba ta ƙaru duk da tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran
Natsuwa da aka samu bayan tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran ya sauya zuwa fargaba a ranar Laraba, yayin da rikici ke ci gaba da ƙamari a yankin, inda Israel ta kaddamar da hare-hare mafi girma zuwa yanzu kan Lebanon, sannan Iran ta kai hari kan cibiyoyin mai na ƙasashen yankin Tekun Fasha.
Kasuwannin kuɗi na duniya sun tashi bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yarjejeniyar a ƙarshen jiya Talata, sa’o’i biyu kafin wa’adin da ya bai wa Iran domin buɗe mashigar Hormuz da aka killace, ko kuma ta fuskanci abin da ya kira lalata “dukkan wayewarta”.
Sai dai duk da cewa Israel da Amurka sun dakatar da hare-hare kan Iran, Isra’ila ta ƙara tsananta yaƙinta na daban a Lebanon, inda ta kaddamar da hare-hare mafi muni zuwa yanzu, lamarin da ya haifar da rudani a Beirut yayin da gine-gine ke rushewa.
Ministan lafiya na Lebanon ya ce mutane da dama sun mutu, yayin da daruruwa suka jikkata. Mazauna yankin sun ce wasu hare-haren Isra’ila sun zo ba tare da gargadin da aka saba bayarwa ga fararen hula domin su tsere ba.
Kamfanin dillancin labarai na Iran, Tasnim News Agency, ya rawaito wata majiya da ba a ambaci sunanta ba na gargadin cewa Iran za ta janye daga tsagaita wuta idan har hare-haren kan Lebanon suka ci gaba.


