Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka
Published: April 8, 2026 at 7:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Fargaba ta ƙaru duk da tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran

Natsuwa da aka samu bayan tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran ya sauya zuwa fargaba a ranar Laraba, yayin da rikici ke ci gaba da ƙamari a yankin, inda Israel ta kaddamar da hare-hare mafi girma zuwa yanzu kan Lebanon, sannan Iran ta kai hari kan cibiyoyin mai na ƙasashen yankin Tekun Fasha.

Kasuwannin kuɗi na duniya sun tashi bayan Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yarjejeniyar a ƙarshen jiya Talata, sa’o’i biyu kafin wa’adin da ya bai wa Iran domin buɗe mashigar Hormuz da aka killace, ko kuma ta fuskanci abin da ya kira lalata “dukkan wayewarta”.

Sai dai duk da cewa Israel da Amurka sun dakatar da hare-hare kan Iran, Isra’ila ta ƙara tsananta yaƙinta na daban a Lebanon, inda ta kaddamar da hare-hare mafi muni zuwa yanzu, lamarin da ya haifar da rudani a Beirut yayin da gine-gine ke rushewa.

Ministan lafiya na Lebanon ya ce mutane da dama sun mutu, yayin da daruruwa suka jikkata. Mazauna yankin sun ce wasu hare-haren Isra’ila sun zo ba tare da gargadin da aka saba bayarwa ga fararen hula domin su tsere ba.

Kamfanin dillancin labarai na Iran, Tasnim News Agency, ya rawaito wata majiya da ba a ambaci sunanta ba na gargadin cewa Iran za ta janye daga tsagaita wuta idan har hare-haren kan Lebanon suka ci gaba.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki
Next Post: An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika
Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Tattalin Arzikin Kasar Uganda Zai Bunkasa A Wannan Shekarar Labarai
Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
  • Majalisa A Kasar Somaliya Ta Amince Da Sauya Tsarin Mulkin Kasar Afrika
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.