Prime Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada jiya Alhamis cewa, yana neman shawarwari kai tsaye da hukumomin Lebanon a Beiruit, kwana daya bayan da Isra’ila ta kai hari mafi muni da bama-bamai tun fara yakin, har ta halaka mutane dari uku, wanda ya jefa yarjejeniyar tsagaita wuta da shugaba Donald Trump ya kulla da Iran, cikin hadari.
Wani jami’in Lebanon ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ita ma Lebanon tana bukatar ta gudanar da shawarwari kai tsaye da Isra’ila na neman a tsagaita wuta, shigen abunda yake gudana tsakanin Iran da Amurka.
Trump ya bayyana shirin tsagaita wuta a yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran da ya shiga mako shida, a daren talata, jim kadan kamin wa’adin da ya bayar ya kure, wanda yayi barazanar zai shafe Iran daga doron kasa.
A Pakistan, hukumomin kasar suna shirye shiryen zaman farko na shawarwari tsakanin Amurka da Iran, tuni har ta rufe wasu hanyoyi a Isalamabad babban birnin kasar.
Sai dai babu wata alamar cewa Iran ta bude mashigin ruwan Hormuz, matakin da ya janyo mummunar kassara jigilar makamashi a tarihi, inda Tehran take nuni da ci gaban hare hare da isra’ila take kai wa a Lebanon , a zaman dalili.
A cikin sa’o’i 24 tun bayan sanarda tsagaita wuta, jirgin ruwa mai dakon daya ne kadai, tare da wasu jirage masu dakon kaya 5 ne suka ratsa ta mashigin ruwa na Hormuz, hanyar da galibi jiragen ruwa 140 suke bi ako wace rana, inda ta nan ne kashi 20 cikin dari na makamashi da duniya ta dogara akai yake bi.


