Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon
Published: April 10, 2026 at 5:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Prime Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya fada jiya Alhamis cewa, yana neman shawarwari kai tsaye da hukumomin Lebanon a Beiruit, kwana daya bayan da Isra’ila ta kai hari mafi muni da bama-bamai tun fara yakin, har ta halaka mutane dari uku, wanda ya jefa yarjejeniyar tsagaita wuta da shugaba Donald Trump ya kulla da Iran, cikin hadari.

Wani jami’in Lebanon ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ita ma Lebanon tana bukatar ta gudanar da shawarwari kai tsaye da Isra’ila na neman a tsagaita wuta, shigen abunda yake gudana tsakanin Iran da Amurka.

Trump ya bayyana shirin tsagaita wuta a yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran da ya shiga mako shida, a daren talata, jim kadan kamin wa’adin da ya bayar ya kure, wanda yayi barazanar zai shafe Iran daga doron kasa.

A Pakistan, hukumomin kasar suna shirye shiryen zaman farko na shawarwari tsakanin Amurka da Iran, tuni har ta rufe wasu hanyoyi a Isalamabad babban birnin kasar.

Sai dai babu wata alamar cewa Iran ta bude mashigin ruwan Hormuz, matakin da ya janyo mummunar kassara jigilar makamashi a tarihi, inda Tehran take nuni da ci gaban hare hare da isra’ila take kai wa a Lebanon , a zaman dalili.

A cikin sa’o’i 24 tun bayan sanarda tsagaita wuta, jirgin ruwa mai dakon daya ne kadai, tare da wasu jirage masu dakon kaya 5 ne suka ratsa ta mashigin ruwa na Hormuz, hanyar da galibi jiragen ruwa 140 suke bi ako wace rana, inda ta nan ne kashi 20 cikin dari na makamashi da duniya ta dogara akai yake bi.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe
Next Post: Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
Zamu Tarwatsa Cibiyoyin Makamashi Da Cibiyoyin Mai Din Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.