Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana aniyar ta na ganin cewa tallafin dala miliyan 500 da Bankin Duniya ya amince da shi, ya isa hannun manoma na hakika a fadin kasar nan, maimakon karkata shi ga akwakun ‘yan siyasa.
Shugaban Hukumar Ba da Tallafin Kuɗaɗen Haɗin Gwiwa na Ƙasa (NFC), Emmanuel Atama, shi ne ya tabbatar da hakan yayin wata hira da aka yi da shi kwanan nan. Atama ya bayyana cewa shirin an tsara shi ne don ya amfani akalla manoma miliyan daya, tare da magance matsalolin da suka dabaibayi shirye-shiryen da suka gabata.
Atama ya bayyana cewa daya daga cikin manyan matsalolin da suka hana tallafin noma tasiri a baya shi ne tsoma bakin siyasa da kuma rashin sahihan bayanai.
“Yawancin shirye-shiryen da aka yi a baya sun fuskanci cikas sakamakon rashin isasshen bayani ga manoma da kuma tsoma bakin yan siyasa, wanda hakan ya hana kuɗaɗen isa ga waɗanda aka yi niyya,” in ji shi.
Ya kara da cewa wannan karon tsarin zai bambanta, musamman sakamakon hadin gwiwa da Ministan Noma mai kwazo, wanda ya nuna shirye-shiryen cire duk wata sarkakiya da ke kawo cikas wajen aiwatar da ayyukan hukumar.
Shugaban ya kuma bayyana cewa tattaunawar da suka yi da Bankin Duniya ta bankado kurakuran da aka tafi da su a shirye-shirye irin su Anchor Borrowers Program. Saboda haka, wannan sabon tsarin zai mayar da hankali ne wajen gyara wadannan kura-kurai.
A halin yanzu, hukumar ta riga ta fara zagaye domin wayar da kan manoma a jihohi daban-daban, inda ake karfafa musu gwiwa su shiga kungiyoyin hadin gwiwa (cooperatives).
Wannan shi ne zai ba da damar tantance su cikin sauki da kuma tabbatar da gaskiya wajen rabon tallafin.
Wani sabon salo da shirin zai zo da shi don toshe kofofin almundahana shi ne raba kayan aikin noma maimakon kudi tsantsa. Atama ya fayyace cewa, Za a fi mayar da hankali wajen samar da takin zamani, iri, da injinan noma. Idan har akwai buƙatar bayar da kudi kai tsaye, ba zai wuce kashi 10% zuwa 15% na jimillar tallafin da manomin zai samu ba.
Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen hauhawar farashin abinci, inda ake fatan wannan tallafi zai bunkasa samar da abinci a fadin Najeriya.


