Gwamnan Kano a Najeriya, Abba Kabir Yusuf ya miƙa sunan Murtala Sule Garo gaban majalisar dokokin jihar domin ta amince ya zama mataimakinsa.
Gwamnan ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa Mustapha Muhammad ya aike wa manema labarai ranar Talata.
Gwamnan ya ce yana so Garo ya maye gurbin Abdulsalam Gwarzo, wanda ya ajiye muƙaminsa a watan Maris.
Masana harkokin siyasa na ganin naɗa Murtala Garo a matsayin mataimakin Gwamna Abba zai iya yin tasiri a zaɓen 2027 inda Gwamna Abba ke neman yin ta-zarce a ƙarƙashin jam’iyyar APC bayan ya fice daga NNPP, matakin da wasu suka bayyana a matsayin cin amanar ubangidan sa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.


