NAHCON Ta Bukaci Mahajjata Su Sayi Dabbobin Hadaya Ta Cibiyoyin Da Aka Amince Da Su Kadai
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta yi kira ga dukkan maniyyatan Najeriya da ke gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 da su tabbatar sun sayi dabbobin Hadaya kadai ta hanyar dandalin Nusuk Masar ko kuma cibiyoyin sayarwa da Hukumar Kula da Ayyukan Hadaya da Adahi ta Masarautar Saudiyya ta amince da su.
Hukumar ta jaddada cewa bai kamata mahajjata su yi hulɗa da mutane ko ƙungiyoyi da ba su da izini ba wajen saye, talla, ko gudanar da duk wani aiki da ya shafi Hadaya da Adahi.
NAHCON ta bayyana cewa wannan mataki an ɗauke shi ne domin kare mahajjata daga zamba, damfara da sauran hanyoyin cutarwa, tare da tabbatar da cewa an kiyaye haƙƙoƙinsu a lokacin gudanar da ibadun Hajji.
Hukumar ta kuma bukaci mahajjata su yi amfani da hanyoyin da aka amince da su kawai domin tabbatar da cewa an gudanar da ibadar Hadaya da Adahi yadda Shari’ar Musulunci ta tanada tare da bin dokoki da ƙa’idojin Masarautar Saudiyya.
Hakazalika, an umarci Hukumomi da Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihohi, Hukumomin Hajji da Umrah, Kwamitocin Alhazai da kuma Kamfanonin Shirya Hajji (Tour Operators) da su wayar da kan mahajjata tare da tabbatar da cikakken bin wannan umarni.
NAHCON ta yi addu’ar Allah Ya karɓi ibadun mahajjata baki ɗaya, Ya ba su Hajji Mabrur, Ya kuma dawo da su gida lafiya.


