Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika

Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
Published: May 26, 2026 at 11:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata babbar kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta yanke hukunci cewa tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, ya cancanci kuma zai iya tsayawa takarar Shugaban Ƙasa a zaɓen shekarar 2027.

Kotun, wadda ke ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Peter Lifu na Babbae Kotun Tarayya da ke Abuja, ta bayyana hukuncin ne a ranar Talata, inda ta tabbatar da cewa babu wani tanadi na doka da ya hana Jonathan sake tsayawa takara.

Wannan hukunci ya biyo bayan shari’ar da wani mai shigar da ƙara, Johnmary Jideobi, ya shigar, yana neman kotu ta hana Jonathan tsayawa takara ko kuma bayyana kansa a matsayin ɗan takara a kowane jam’iyya a zaɓen 2027.

A cikin ƙarar, mai shigar da ƙara ya kuma nemi kotu ta hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, Independent National Electoral Commission, karɓa, sarrafawa ko bayyana sunan Jonathan a matsayin ɗan takara.

Sai dai mai shari’a Peter Lifu ya yi watsi da waɗannan buƙatu, inda ya bayyana cewa Jonathan na da cikakken haƙƙi a ƙarƙashin kundin tsarin mulki na 1999 da aka gyara, domin shiga takarar shugaban ƙasa.

Hukuncin kotun ya kuma zo ne a daidai lokacin da wani ɓangare na jam’iyyar PDP, ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, ya bayar da rangwame (waiver) ga Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar.

Jonathan, wanda ya mulki Najeriya daga shekarar 2010 zuwa 2015, ya sha kaye a zaɓen 2015 a hannun Muhammadu Buhari, lamarin da ya zama tarihi a siyasar ƙasar saboda shi ne shugaban ƙasa na farko da ya amince da shan kaye a zaɓen sake tsayawa mulki.

Hukuncin kotun na zuwa ne a matsayin wani muhimmin sauyi da ka iya ƙara ƙaimi a tseren siyasar 2027 da ake tunkara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
Next Post: Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP

Karin Labarai Masu Alaka

Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
Rikicin Siyasa A Jihar Rivers Sakamakon Ayyana Fubara A Matsayin Shugaban APC Siyasa
Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gudanar Da Tiyatar Ido Kyauta A Gombe Afrika
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.