Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
Published: June 4, 2026 at 4:31 PM | By: Bala Hassan

Jose Mourinho ya ƙara ta’azzara takaddamarsa da hukumomin ƙwallon ƙafa na Turkiyya ta hanyar shigar da ƙara a hukumance ga Kotun Kare Hakkin Bil Adama ta Turai (ECHR).

Ɗan ƙasar Portugal ɗin, wanda ake sa ran zai koma ƙungiyar kwallon kafa ta Real Madrid da ke Spain bayan zaɓen shugaban da za a yi a ƙungiyar, ya yi zargin cewa an take masa haƙƙinsa na a lokacin da yake tare da Fenerbahce.

Mourinho Bayan ya bar Fenerbahce a watan Agusta na 2025, ya nemi ECHR a Strasbourg don ƙalubalantar takunkumin ladabtarwa da Hukumar Kwallon Kafa ta Turkiyya (TFF) ta sanya masa.

Shari’ar da aka shigar ta mayar da hankali ne kan martanin da Mourinho ya mayar bayan nasarar da Fenerbahce ta samu a kan Trabzonspor a watan Nuwamba na 2024.

In da aka mishi haramcin wasa ɗaya da kuma tara mai yawa daga hukumomi saboda sukar VAR da hukumomin ƙwallon ƙafa na Turkiyya.

An ci gaba da ɗaukar matakin takunkumin bayan da aka dakatar da daukaka ƙarar kocin, wanda hakan ya sa kocin mai shekaru 63 ya nemi shigar da tasa a kotunan ƙasa da ƙasa.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
Next Post: JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.