Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika

Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
Published: June 16, 2026 at 1:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin Kungiyar Kiristoci a Arewacin Najeriya sun miƙa saƙonnin taya murna ga Musulmi a Najeriya da ma duniya baki ɗaya, bisa shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci (Hijira 1448), inda suka jaddada muhimmancin zaman lafiya, jituwa da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai.

Sun kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta yi la’akari da ayyana ranar Sabuwar Shekarar Musulunci a matsayin ranar hutu ta ƙasa, domin bai wa Musulmi damar gudanar da bukukuwan su cikin natsuwa da tunani.

Shugaban Majami’ar Christ Evangelical and Life Intervention Ministry da ke Kaduna, Pastor Yohanna Buru, ya taya Musulmi murna, tare da kiran a ƙara yin addu’o’in zaman lafiya da haɗin kai a Najeriya da yankin Yammacin Afirka baki ɗaya.

A yayin ziyararsa ga wasu malaman Musulunci, Pasto Buru ya ce wannan na daga cikin ƙoƙarinsa na ƙarfafa dangantakar addinai da inganta zaman lafiya tsakanin Kirista da Musulmi a jihar Kaduna da ƙasar baki ɗaya.

Ya ce ya saba amfani da kafafen sada zumunta wajen aika saƙonnin zaman lafiya a duk Sabuwar Shekarar Musulunci, domin taya abokansa Musulmi murna tare da yi musu fatan alheri.

Ya kuma buƙaci al’ummar Jihar Kaduna da su ci gaba da zama cikin zaman lafiya, tare da goyon bayan matakan gwamnati na ƙarfafa haɗin kai da daidaito a ƙasa.

“Nigeriyawa su riƙa nuna haƙuri da yafiya, su kuma mara wa gwamnati baya wajen ƙoƙarin tabbatar da haɗin kai na ƙasa da magance matsalolin da suka shafi ƙabilanci, siyasa da addini,” in ji shi.

A nasa jawabin, Pasto John Immanuel ya yi kira ga mazauna Kudancin Kaduna da su ƙara rungumar zaman lafiya da fahimtar juna.

Ya kuma taya Musulmi murna, tare da yin addu’ar Allah ya kawo ƙarshen matsalolin tsaro da ke ci gaba da addabar sassan Arewacin Najeriya.

A wani ɓangare kuma, wasu malaman Musulunci, Mallam Idris Musa da Liman Ilyasu Husaine, sun nuna godiya ga shugabannin Kiristoci bisa saƙonnin goyon baya da fatan alheri da suka aiko.

Sun ce bikin Sabuwar Shekarar Musulunci ba na Musulmi kaɗai ba ne, illa na dukkan bil’adama, domin yana ɗauke da saƙon zaman lafiya da juna.

A ranar Talata 16 ga Yuni, 2026, daidai 1 ga Muharram 1447, ne ake fara sabuwar shekarar Musulunci, bisa ganin jinjirin wata.

Sabuwar Shekarar Musulunci na tunawa da Hijirar Manzon Allah (SAW) daga Makka zuwa Madina, wadda ke da matuƙar muhimmanci a tarihin Musulunci.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
  • Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.