Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Bayan Rikicin Manoma Da Makiyaya, Kwamitin White Paper Ya Ziyarci Bojude Da Kwami
Published: July 15, 2026 at 6:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta sake jaddada aniyarta na tabbatar da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya ta hanyar ƙarfafa matakan kare hanyoyin kiwo da kuma dazukan kiwo domin rage rikice-rikicen da ke faruwa tsakanin bangarorin biyu.

Wannan na ƙunshe ne cikin ziyarar duba aiki da Ƙaramin Kwamitin Aiwatar da Rahoton White Paper kan Hanyoyin Kiwo ya kai garin Jauro Jibir da ke Kwami, gundumar Bojude, da kuma Filin Kiwo na Ƙasa da Ƙasa na Kwalale da ke yankin Daban Fulani a jihar Gombe

Da yake jawabi ga al’ummar yankunan, ɗaya daga cikin mambobin kwamitin, Ardo Chindo Abubakar, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta umarci jama’a, musamman manoma, da su guji noma a cikin hanyoyin kiwo da filayen kiwo da aka keɓe domin wannan manufa.

Ya ce filayen kiwo mallakin Gwamnatin jihar Gombe ne, kuma an ware su ne domin kiwon dabbobi, yana mai cewa kiyaye su zai taimaka wajen rage rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A nasa jawabin, Hakimin Bojude, Alhaji Ibrahim Dan Buram, da Hakimin Daban Fulani, Alhaji Muhammad Seyo, sun buƙaci al’ummominsu da su mara wa manufofin gwamnatin jihar baya tare da bai wa Kwamitin Aiwatar da Rahoton White Paper cikakken haɗin kai domin cimma nasarar aikin da aka ɗora masa.

Hakiman sun kuma shawarci jama’a da su kasance masu bin doka da oda, su guji duk wani abu da ka iya kawo tashin hankali ko ɓata sunan al’ummominsu da addininsu.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kwami, wanda shugaban Sashen Noma na ƙaramar hukumar, Muhammad Ibrahim Bojude, ya wakilta, ya yi kira ga jama’a, musamman manoma da makiyaya, da su mutunta dokokin da suka shafi hanyoyin kiwo tare da ba kwamitin cikakken goyon baya da haɗin kai.

Ya ce haɗin kan gwamnati, sarakunan gargajiya, manoma da makiyaya zai taimaka matuƙa wajen samar da zaman lafiya da bunƙasa harkokin noma da kiwo a Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027
Next Post: Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Feyenoord Ta Fara Tattaunawa Da Manchester United Kan Daukar Chido Obi Aro  Wasanni
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Kuɗaɗen Da EFCC Ta Kwato Za Su Tallafa Wa Shirin Lamunin Karatu Afrika
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.