Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

‘Yan Sandan Gombe Sun Yi Taron Gaggawa Da Jam’iyyun Siyasa Da INEC Kan Tsaro
Published: July 18, 2026 at 2:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe ta gudanar da wani taron gaggawa kan harkokin tsaro tare da shugabannin jam’iyyun siyasa da wakilan Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), domin tattauna yadda za a tabbatar da zaman lafiya gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

An gudanar da taron ne a babban ɗakin taro na Rundunar, sakamakon ƙarin damuwa kan yawaitar laifukan da ke da alaƙa da siyasa, musamman amfani da ‘yan daba wajen tayar da tarzoma, yayin da harkokin siyasa ke ƙara ɗaukar zafi kafin lokacin yaƙin neman zaɓe.

Da yake maraba da mahalarta taron, Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya ce an kira taron ne bayan bayanan sirri sun nuna alamun ƙaruwa a ayyukan tashin hankali masu nasaba da siyasa tun kafin fara yaƙin neman zaɓe a hukumance.

Ya bayyana cewa matsalar Kalare da ake fuskanta a jihar, tare da nauyin da ya rataya a wuyan Rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, sun sa ya zama dole a haɗa masu ruwa da tsaki domin nemo mafita.

Kwamishinan ya buƙaci mahalarta taron su bayar da shawarwari masu amfani domin tabbatar da zaman lafiya, yana mai jaddada cewa lokaci mafi dacewa na dakile rashin tsaro shi ne kafin ya rikide ya gagari shawo kansa.

Shi ma da yake jawabi, Daraktan Hukumar Tsaro ta DSS a jihar Gombe, Haruna Nuhu, tare da Kwamandan Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula (NSCDC), sun bayyana taron a matsayin abin a yaba da shi kuma mai matuƙar muhimmanci.

Sun ce irin wannan zama zai ƙara bai wa hukumomin tsaro damar sa ido kan harkokin siyasa tare da tabbatar da bin dokokin zaɓe, suna mai cewa, “Idan za a yi wasan siyasa, dole ne a yi shi bisa ƙa’idoji da dokokin da aka tanada.”

A nata jawabin, Shugabar Sashen Wayar da Kan Masu Zaɓe ta INEC a Jihar Gombe, Misis Rifqatu Maxwell, ta bayyana cewa har yanzu Hukumar ba ta amince da fara yaƙin neman zaɓe ba.

Ta sanar da cewa yaƙin neman zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa zai fara ne a ranar 19 ga Agustan 2026, yayin da na Gwamna zai fara a ranar 9 ga Satumban 2026.

Ta yi kira ga jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu da su bi ƙa’idojin INEC ba tare da karya doka ba, tana mai gargaɗin cewa duk wanda ya saɓa zai fuskanci hukuncin doka.

Shugabannin jam’iyyun siyasa da suka halarci taron sun yi alƙawarin aiwatar da matsayar da aka cimma domin tabbatar da gudanar da siyasa cikin lumana.

Daga cikin waɗanda suka gabatar da jawabai akwai Manjo Janar A. K. Kwaskebe, Adamu H. Garba, Benjamin Sati, mai ba jam’iyyar PDP shawara kan harkokin shari’a, Lawan Maigoro na Jam’iyyar Labour Party da Bobo Benson Abubakar na Jam’iyyar Action Alliance.

Masu jawabin sun kuma buƙaci a magance tushen rikice-rikicen zaɓe, ciki har da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi, zargin nuna son kai wajen aiwatar da dokokin zaɓe da kuma tabbatar da hukunta masu aikata laifukan zaɓe.

A nasa gudunmawar, wani Wakilin kafar yada labarai ya nuna damuwa kan ƙaruwar cin zarafi ta kafafen sada zumunta da yaɗa bayanan ƙarya a lokutan siyasa.

Ya buƙaci a ɗauki matakan kariya, ciki har da yin rajistar masu kula da kafafen yaɗa labarai na jam’iyyun siyasa da ‘yan takara a INEC, tare da tsaurara aiwatar da Dokar Laifukan Yanar Gizo (Cybercrimes Act).

A ƙarshen taron, Kwamishinan ‘Yan Sandan ya gode wa mahalarta bisa gudunmawar da suka bayar, ya kuma yi bayani kan wasu daga cikin batutuwan da aka taso da su kafin a rufe taron da ɗaukar hoton haɗin gwiwa.

Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers
Next Post: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Rantsar Da Sabon Shugaban Ma’aikatan Jiha da Kwamishinoni 23

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.