Ƙungiyar Fulani ta Miyetti Allah Kautal Hore a jihar Gombe ta bayyana goyon bayanta ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna, wanda aka fi sani da Sardaunan Gombe, a matsayin ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC a zaɓen shekarar 2027

Shugaban ƙungiyar a jihar, Ardo Chindo Abubakar, ne ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da makiyaya da manoma a Masarautar Bojude da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.
Taron ya gudana ne a lokacin da tawagar yaƙin neman goyon bayan Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna ƙarƙashin jagorancin Dakta Ahmad Muhammad Gana ta kai ziyara yankin
Ardo Chindo ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma tare da samar da mafita ga rikice-rikicen da suka daɗe suna faruwa tsakanin al’ummomin Fulani a yankin. Ya kuma buƙaci mazauna yankin su ci gaba da zama lafiya domin samun ci gaba mai ɗorewa.
Da yake jawabi, jagoran tawagar yaƙin neman goyon baya, Dakta Ahmad Gana, ya bayyana Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin mutum mai tawali’u, tausayi da ƙwarewa wajen gudanar da aiki. Ya ce ya taimaka wa mutane da dama a lokacin da yake aiki a Hukumar Samar da Ruwa ta Jihar Gombe da kuma Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO).
Ya yi kira ga al’ummar jihar Gombe da su marawa Dakta Gwamna baya, yana mai cewa jajircewarsa, gaskiyarsa da sadaukarwarsa wajen taimakon talakawa sun cancanci a ba shi damar jagorantar jihar.
Shi ma Shugaban Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma (Kwami West LCDA), Sa’ad Abdulmumini, ya bayyana cikakken goyon bayansa ga jam’iyyar APC da ‘yan takararta, yana mai cewa ayyukan ci gaban da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya aiwatar sun ƙara wa jam’iyyar karɓuwa a wajen al’umma.
A nasa jawabin, Hakimin Bojude, Alhaji Muhammad Ibrahim Dan Buram, ya lissafo wasu ayyukan raya ƙasa da aka aiwatar a masarautarsa, ciki har da gina fadar hakimi, hanyoyi, fitilun tituna masu amfani da hasken rana da kuma kafa hedikwatar Hukumar Ci Gaban Ƙaramar Hukumar Kwami ta Yamma a Bojude.

Hakimin ya sake jaddada goyon bayansa ga Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna da sauran ‘yan takarar APC, yana mai bayyana fatan cewa za su ci gaba da kawo ribar dimokuraɗiyya ga al’ummar Jihar Gombe.


