Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa abin da ya bayyana a matsayin jajircewarsa wajen jagorantar Najeriya da kuma ƙoƙarin magance matsalolin tsaro, musamman hare-haren da ke shafar wasu al’ummomin Kiristoci.
A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026 da ya aike wa Shugaba Tinubu, Trump ya yaba da ƙudurin shugaban na yaƙi da ta’addanci tare da tabbatar da cewa Amurka za ta ci gaba da mara wa Najeriya baya wajen inganta tsaro da tabbatar da zaman lafiya.
Trump ya ce abin alfahari ne gare shi ya tsaya tare da Shugaba Tinubu wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwar ƙasashen biyu zai taimaka wajen ƙarfafa Najeriya da bunƙasa tattalin arzikinta.
Shugaban na Amurka ya ce Najeriya da Amurka suna da manufar bai ɗaya ta yaƙi da ta’addanci a yankin Yammacin Afirka, yana mai nuni da cewa Tsarin Haɗin Gwiwar Tsaro na Amurka da Najeriya na shekarar 2026 ya samar da ingantaccen tubali na zurfafa haɗin gwiwar soji tsakanin ƙasashen biyu.
Ya kuma bayyana cewa Amurka ta tura jami’an rundunar musamman domin horas da sojojin Najeriya tare da ba su ƙwarewa, bayanan sirri da sauran tallafin da za su taimaka wajen yaƙi da ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Trump ya kuma bayyana fatan ci gaba da tattaunawa da Shugaba Tinubu domin ƙara bunƙasa alaƙar da ke tsakanin Najeriya da Amurka.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar.


