Wata fashewa ta afku yayin da ake zargin mayakan Boko Haram sun kai hari kan ayarin ɗan takarar gwamnan jihar Borno na jam’iyyar APC, Engr. Mustapha Gubio.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a hanyar Gubio–Kareto–Damasak, lokacin da Gubio da tawagarsa ke dawowa Maiduguri a arewacin Najeriya
An ce wata motar jami’an tsaro da ke jagorantar ayarin ta taka wani abin fashewa da aka binne a hanya, lamarin da ya haddasa fashewar.
Bayan haka, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji, ’yan sanda da ’yan kungiyar CJTF sun yi artabu da maharan, inda suka tilasta musu ja da baya.
Rahotannin sun ce babu wanda ya mutu ko ya jikkata a cikin ayarin, sai dai motar jami’an tsaron ta samu mummunar barna.
Ana ci gaba da jiran ƙarin bayani daga hukumomin tsaro.


