Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gombe Ta Zo Ta Biyu Wajen Aiwatar Da Shirin L-PRES
Published: September 5, 2026 at 7:06 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shirin Ƙara Ingancin Kiwo da Juriya na L-PRES a jihar Gombe ya ƙarfafa haɗin gwiwa da sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Kiwo ta jihar, domin ƙara inganta ayyukan da ake gudanarwa da kuma hanzarta aiwatar da ajandar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ta sauya fasalin harkar kiwo a jihar.

Mai Gudanar da Shirin L-PRES na jihar Gombe, Farfesa Usman Bello Abubakar, ne ya bayyana hakan lokacin da ya jagoranci tawagar shirin zuwa ziyarar sanayya ga Kwamishinan Bunƙasa Kiwo, Hon. Salihu Baba Alkali.

Farfesa Abubakar ya ce ziyarar ta kasance ne domin yi wa kwamishinan bayani kan manufofi, ayyuka da nasarorin da shirin L-PRES ya samu tun bayan fara aiki a jihar, tare da gano hanyoyin ƙara haɗin gwiwa da sabuwar ma’aikatar.

Ya bayyana cewa L-PRES shiri ne na tsawon shekaru shida da Bankin Duniya ke tallafawa, wanda jihar Gombe ta shiga a watan Disambar 2023, da nufin inganta samar da amfanin dabbobi, ƙara juriya da bunƙasa kasuwancin kayayyakin kiwo.

A cewarsa, shirin ya aiwatar da wasu muhimman ayyuka da suka shafi samar da ruwa, kasuwannin dabbobi, kiwon shanu, lafiyar dabbobi, da kuma rage rikice-rikicen manoma da makiyaya musamman a hanyoyin shanu da wuraren kiwo.

Ya ce zuwa yanzu L-PRES ya gina rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana sama da 100, ya gyara madatsun ruwa na gargajiya, sannan ya kafa ƙungiyoyin manoman kiwo da cibiyoyin tattara madarar shanu guda 55.

Ya ƙara da cewa shirin na samar da horo, ingantattun nau’o’in dabbobi da sauran tallafi domin ƙara yawan amfanin kiwo da ribar da manoma da masu kiwo ke samu.

Farfesa Abubakar ya kuma bayyana nasarar da shirin cusa maniyyin shanu, wato Artificial Insemination, ya samu, inda aka samu kashi 79 cikin 100 na nasarar samun ciki da kuma kashi 66 cikin 100 na haihuwa.

Ya ce wannan nasara ta sa jihar Gombe ta samu karɓuwa a matsayin abin koyi ga sauran jihohi, yayin da ake gina Cibiyar Cusa Maniyyi da Yawaita Ingantattun Nau’o’in Dabbobi a tsangayar Noma ta Jami’ar Jihar Gombe da ke Mallam Sidi.

Mai Gudanar da Shirin ya ce L-PRES na kuma tallafa wa ayyukan dakile rikice-rikice ta hanyar sake tsara da taswirar hanyoyin kiwo da wuraren kiwo, kafa wuraren hutawar dabbobi, da kuma shiga cikin kwamitocin rigakafi da sasanta rikice-rikicen manoma da makiyaya a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

Ya bayyana cewa shirin na zuba jari wajen sarrafa amfanin dabbobi a cikin gida, ciki har da gina katafaren mayanka na zamani, cibiyoyin kiwon kaji da kitso, masana’antar fata da kayayyakin fata, da kuma kasuwar dabbobi ta ƙasa da ƙasa a yankin bunƙasa harkar noma da kiwo na Gombe.

Game da lafiyar dabbobi kuwa, ya ce ana gyarawa da inganta cibiyoyin kula da lafiyar dabbobi, tare da kafa dakunan gwaje-gwajen sa ido kan cututtuka da wuraren adana allurai cikin yanayin sanyi, baya ga tallafa wa shirye-shiryen yi wa dabbobi allurar rigakafi.

Farfesa Abubakar ya kuma bayyana cewa jihar Gombe ta zo ta biyu wajen gudanarwa da aiwatar da shirin L-PRES, lamarin da ya sanya wasu jihohi ke nuna sha’awar koyon darussa daga irin nasarorin da Gombe ta samu.

Da yake mayar da martani, Kwamishinan Bunƙasa Kiwo na jihar Gombe, Hon. Salihu Baba Alkali, ya yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa hangen nesansa da jajircewarsa wajen aiwatar da manyan ayyukan raya jihar.

Kwamishinan ya kuma taya ofishin gudanar da shirin L-PRES murnar nasarorin da ya samu, yana mai jaddada muhimmancin ci gaba da kiyaye inganci wajen aiwatar da ayyukan.

Ya ce kafa Ma’aikatar Bunƙasa Kiwo na da nufin ƙarfafa da kuma bunƙasa nasarorin da aka samu a fannin kiwo, musamman ta hanyar shirye-shirye irin na L-PRES.

Hon. Alkali ya ce samar da wadataccen abinci, ƙirƙirar ayyukan yi, rigakafi da sasanta rikice-rikicen manoma da makiyaya, da farfaɗo da ababen more rayuwa na kiwon dabbobi, musamman shirin cusa maniyyin shanu, na daga cikin abubuwan da ma’aikatar ta sanya a gaba.

Kwamishinan ya tabbatar wa tawagar L-PRES cewa ma’aikatar za ta ci gaba da ba shirin goyon baya tare da ƙarfafa haɗin gwiwa, wayar da kan jama’a da kuma ilmantar da su, domin tabbatar da cewa al’ummar jihar sun fahimci shirye-shiryen tare da amfana da su.

Ya bayyana kyakkyawan fata cewa ƙara haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatar da L-PRES zai taimaka wajen faɗaɗa tasirin shirye-shiryen kiwo, samar da wadataccen abinci, ƙirƙirar ayyukan yi da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar Gombe.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rikicin Aure: Albani Agege Ya Zargi Sheikh Gumi Da Boye Matarsa ‘Yar Morocco
Next Post: ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika
‘Yan Sandan Gombe Sun Yi Taron Gaggawa Da Jam’iyyun Siyasa Da INEC Kan Tsaro Labarai
Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.