Wani mazaunin jihar Kaduna kuma Shugaban tawagar Qausain Alhaji Nasiru Musa Idris (Albani Agege) ya zargi fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi, da raba shi da matarsa ‘yar kasar Morocco, wadda ya ce ta kwashe kusan watanni 11 ba tare da ya samu damar tuntubarta ba.
Nasir Albani Agege ya bayyana hakan ne a wata hira da RFI Hausa, inda ya ce ya kai matarsa wajen Sheikh Gumi ne domin ba ta shawarar addini, bayan malamin ya bukaci ya kawo masa ita.
Ya ce kafin wannan lokaci, ya amince da Sheikh Gumi a matsayinsa na malamin addini, shi ya sa bai ga wani laifi ba wajen kai matarsa gare shi domin neman shawara.
A cewarsa, bayan matar tasa ta gana da Sheikh Gumi, ta daina amsa kiransa, lamarin da ya ce ya sa ya fara kokarin gano inda take tare da neman taimakon hukumomin tsaro.
Idris Albani Agege ya kuma yi zargin cewa kokarin da hukumomin tsaro suka yi na binciken lamarin ya fuskanci cikas.
Ya ce matarsa ba ta taba sanin Sheikh Gumi ba kafin ya gabatar da ita gare shi, yana mai cewa shi ne kadai ya san malamin kuma ya kai ta wajen Gumi ne saboda ya amince da shi.
Haka kuma, Idris ya ce matsalar ta fara ne bayan Sheikh Gumi ya bukaci ya sake samun wata takardar aure daga kotun Shari’a, duk da cewa yana da takardun aure da aka bayar a Morocco da Najeriya.
Ya ce ya gabatar da takardun da suka shafi aurensu, ciki har da wasu takardu daga Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya da ofishin jakadancin Najeriya a Morocco, da kuma rahoton binciken halayyar mutum daga ‘yan sanda.
Idris ya kara da cewa daga bisani ya yi zargin cewa Sheikh Gumi ya fara kokarin ganin an raba auren, tare da cewa ya nemi malamin da ya amsa gayyatar ‘yan sanda domin a gudanar da bincike kan lamarin.
Sai dai Sheikh Ahmad Gumi ya musanta zargin.
Da yake magana da Daily Trust, Sheikh Gumi ya ce matar ta riga ta bar Najeriya, kuma tana kasar Morocco tare da iyayenta cikin kwanciyar hankali.
Malamin ya kuma ce ba ya son yin karin bayani kan lamarin saboda batun yana gaban kotu, amma ya yi barazanar kai Albani Agege kotu bisa zargin bata masa suna.
Shi ma Nasiru Ayuba, wanda aka fi sani da Dan Agaji, kuma mataimaki na musamman na Sheikh Gumi, ya musanta zargin cewa malamin ya tsare matar a gidansa.
Ayuba ya ce matar ce da kanta ta je wajen Sheikh Gumi domin neman taimako kan wata matsala ta kashin kanta, inda malamin ya yi kokarin taimaka mata tare da kai lamarin gaban kotu.
Ya kuma zargi Idris da kokarin bata sunan Sheikh Gumi ta kafafen sada zumunta.
A halin yanzu, lamarin ya zama rikici tsakanin bangarorin biyu, yayin da Idris ke neman a gudanar da bincike kan inda matarsa take da kuma yadda aka raba su, shi kuma Sheikh Gumi ya musanta zargin tare da cewa zai dauki matakin shari’a kan zargin bata masa suna.


