Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Published: December 18, 2025 at 8:25 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasar China ta ce tana adawa da matakin nuna fin karfi, bayan Amurka ta bada umurnin tare dukkan jiragen ruwan jigilar mai da aka kafa ma takunkumi wadanda ke kokarin zuwa ko fitowa daga kasar venezuela mai arzikin man fetur.

China ita ce ta fi kowace kasa sayen danyen man kasar Venezuela, inda a wannan watan ake sa ran cewa a kowace rana zata na saye ganga dubu 600 na man Venezuela.

Ministan harkokin wajen China, Wang Yi, ya fadawa takwaransa na Venezuela a tattaunawar da suka yi ta wayar tarho cewa China tana yin adawa da duk wani matakin nuna fin karfi da wata kasa zata so nunawa, sannan tana goyon bayan kasashe wajen kare mutuncin kasarsu.

Wang bai ambaci sunan Amurka ko shugaba Trump a bayanin da aka bayar na tattaunawar ba, haka kuma bai fadi irin tallafin da China zata iya ba Venezuela ba.

Shugaba Nicolas Maduro yace Amurka tana neman mallakar danyen man fetur na Venezuela ne, kuma girke sojojin da take yi a yankin na neman hambarar da shi daga kan mulki ne.

Amurka dai ta ce tana yakar safarar muggan kwayoyi ne zuwa cikin kasarta.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku
Next Post: Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka
Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.