Amurka tana burin tantance farar fata ‘yan Afirka ta kudu dubu 4,500 ko wani wata a zaman ‘yan gudun hijira zuwa Amurka, adadin ya haura yawan bakin haure da Amurka zata karba a shekara da gwamnatin shugaba Trump ta fada, har ma an girke karin rumfuna ko ofisoshi na wucin gadi a harabar ofishin jakadancin Amurka a Pretoria domin talafawa wannan shiri, kamar yadda bayanai da suke kunshe a takardun kwantiragin wannan aiki suka nuna.
Wannan sabon yunkurin, da ba’a bada sanarwa akai ba dake kunshe cikin wata kasidar ma’aikatar harkokin wajen Amurka mai kwanan watan 27 ga watan Janairu, ya nuna kokarin zafafa shigo da farar fata ‘yan Afirka ta kudun, yayinda Amurkan ta takaita ‘yan gudun hijira daga wasu kasashe.
Shugaba Trump, yace Amurka zata karbi ‘yan gudun hijira 7,500 kadai daga ko ina fadin duniya a bana, yayinda shawarwarin gwamnatin Amurka bara ya nuna kasar tana shirin zata karbi ‘yan gudun hijira dubu 40 ko fi. Zuwa yanzu dai farar fata ‘yan Afirka ta kudu dubu biyu ne suka shigo Amukra zuwa 31 ga watan Janairun bana.
Ahalinda ake ciki, Amurkan ta dakatar da shirin karbar ‘yan gudun hijiran ciki harda farar fata daga Afirka ta kudun.


