Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Published: December 17, 2025 at 2:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe a Najeriya ta sanar da cewa mutum 11 sun kamu da zazzabin Lassa, inda mutum ɗaya ya rasu.

Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya a Jihar Gombe, Dokta Habu, ne ya bayyana hakan yayin wani taron saka ido da mayar da martani kan barkewar cututtuka da aka gudanar a Gombe.

Dokta Habu ya ce marigayin ya fara nuna alamun zazzabin Lassa ne yayin da yake jihar Taraba, kafin daga bisani a turo shi Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Gombe, domin jinya.

Ya kara da cewa, ta fuskar kididdigar lafiyar jama’a, lamarin ana daukarsa a matsayin na jihar Taraba.

“An kula da marasa lafiyar a Gombe, amma asalin zazzabin daga Taraba ya fito, an mayar da lambar EPID zuwa jihar Taraba,” in ji shi.

Ya bayyana cewa yawancin mutanen da aka tabbatar sun kamu da zazzabin Lassa na daga cikin mutanen da ke zuwa jihar Taraba domin aikin noma.

Kwamishinan ya jaddada cewa ko da mutum guda ne aka tabbatar ya kamu da cutar, ana daukar sa a matsayin barkewar cuta, saboda tsananin hadarinta.

Dokta Habu ya ce Gombe ta samu nasarar dakile barkewar cututtuka da dama sakamakon shiri tun kafin lokaci, tare da saurin daukar mataki da hadin gwiwa da hukumomi kamar Hukumar Kula da Cututtuka ta Kasa (NCDC), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF.

Ya ce an kira taron yankin ne domin karfafa tsarin sa ido da daukar mataki kan barkewar cututtuka a jihohin yankin, biyo bayan yawaitar barkewar cututtuka a jihohin Adamawa, Taraba, Bauchi da Plateau.

A karshe, kwamishinan ya bukaci a rika gano cututtuka da wuri, bayar da rahoto cikin gaggawa, da karfafa hadin kai tsakanin jihohi, domin dakile yaduwar zazzabin Lassa da sauran cututtuka masu yaduwa a cikin al’umma

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Next Post: Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.