Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Published: December 17, 2025 at 2:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe a Najeriya ta sanar da cewa mutum 11 sun kamu da zazzabin Lassa, inda mutum ɗaya ya rasu.

Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya a Jihar Gombe, Dokta Habu, ne ya bayyana hakan yayin wani taron saka ido da mayar da martani kan barkewar cututtuka da aka gudanar a Gombe.

Dokta Habu ya ce marigayin ya fara nuna alamun zazzabin Lassa ne yayin da yake jihar Taraba, kafin daga bisani a turo shi Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Gombe, domin jinya.

Ya kara da cewa, ta fuskar kididdigar lafiyar jama’a, lamarin ana daukarsa a matsayin na jihar Taraba.

“An kula da marasa lafiyar a Gombe, amma asalin zazzabin daga Taraba ya fito, an mayar da lambar EPID zuwa jihar Taraba,” in ji shi.

Ya bayyana cewa yawancin mutanen da aka tabbatar sun kamu da zazzabin Lassa na daga cikin mutanen da ke zuwa jihar Taraba domin aikin noma.

Kwamishinan ya jaddada cewa ko da mutum guda ne aka tabbatar ya kamu da cutar, ana daukar sa a matsayin barkewar cuta, saboda tsananin hadarinta.

Dokta Habu ya ce Gombe ta samu nasarar dakile barkewar cututtuka da dama sakamakon shiri tun kafin lokaci, tare da saurin daukar mataki da hadin gwiwa da hukumomi kamar Hukumar Kula da Cututtuka ta Kasa (NCDC), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF.

Ya ce an kira taron yankin ne domin karfafa tsarin sa ido da daukar mataki kan barkewar cututtuka a jihohin yankin, biyo bayan yawaitar barkewar cututtuka a jihohin Adamawa, Taraba, Bauchi da Plateau.

A karshe, kwamishinan ya bukaci a rika gano cututtuka da wuri, bayar da rahoto cikin gaggawa, da karfafa hadin kai tsakanin jihohi, domin dakile yaduwar zazzabin Lassa da sauran cututtuka masu yaduwa a cikin al’umma

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Next Post: Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
  • Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai
  • Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.