Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Published: December 17, 2025 at 2:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe a Najeriya ta sanar da cewa mutum 11 sun kamu da zazzabin Lassa, inda mutum ɗaya ya rasu.

Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya a Jihar Gombe, Dokta Habu, ne ya bayyana hakan yayin wani taron saka ido da mayar da martani kan barkewar cututtuka da aka gudanar a Gombe.

Dokta Habu ya ce marigayin ya fara nuna alamun zazzabin Lassa ne yayin da yake jihar Taraba, kafin daga bisani a turo shi Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Gombe, domin jinya.

Ya kara da cewa, ta fuskar kididdigar lafiyar jama’a, lamarin ana daukarsa a matsayin na jihar Taraba.

“An kula da marasa lafiyar a Gombe, amma asalin zazzabin daga Taraba ya fito, an mayar da lambar EPID zuwa jihar Taraba,” in ji shi.

Ya bayyana cewa yawancin mutanen da aka tabbatar sun kamu da zazzabin Lassa na daga cikin mutanen da ke zuwa jihar Taraba domin aikin noma.

Kwamishinan ya jaddada cewa ko da mutum guda ne aka tabbatar ya kamu da cutar, ana daukar sa a matsayin barkewar cuta, saboda tsananin hadarinta.

Dokta Habu ya ce Gombe ta samu nasarar dakile barkewar cututtuka da dama sakamakon shiri tun kafin lokaci, tare da saurin daukar mataki da hadin gwiwa da hukumomi kamar Hukumar Kula da Cututtuka ta Kasa (NCDC), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF.

Ya ce an kira taron yankin ne domin karfafa tsarin sa ido da daukar mataki kan barkewar cututtuka a jihohin yankin, biyo bayan yawaitar barkewar cututtuka a jihohin Adamawa, Taraba, Bauchi da Plateau.

A karshe, kwamishinan ya bukaci a rika gano cututtuka da wuri, bayar da rahoto cikin gaggawa, da karfafa hadin kai tsakanin jihohi, domin dakile yaduwar zazzabin Lassa da sauran cututtuka masu yaduwa a cikin al’umma

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Next Post: Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
  • Ukraine Ta Mika Wa Amurka Daftarin Yarjejeniya Da Rasha Sauran Duniya
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
  • Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.