Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa
Published: December 9, 2025 at 7:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙungiyar Gwamnonin jihohin arewa ta Naɗa Ezekiel Gomos a matsayin babban darakta don karfafa haɗin kan yankin

Kungiyar gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta amince da naɗin Mista Ezekiel Gomos, OFR, a matsayin Babban daraktan sakatariyar ƙungiyar.

Naɗin dai ya yi daidai da sabbin alƙawuran da ƙungiyar ta ɗauka na ƙarfafa ayyukan hukumominta da inganta haɗin kai a tsakanin jihohin Arewa 19 wajen tinkarar ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

A cewar ƙungiyar, samar da ofishin Babban Daraktan wani kyakkyawan mataki ne na mayar da Sakatariyar ya zuwa cibiya mai inganci wajen haɗa kai da inganta manufofi, da aiki tare da kuma samar da tsare-tsaren ci gaba na dogon zango.

Mista Gomos, wadda tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Filato ne, ƙwararre ne a fannin tattalin arziƙi, siyasa da aikin gwamnati, da kuma inganta harkokin mulki, da bunƙasa kamfanoni masu zaman kansu da kuma ciyar da jama’a gaba.

Ƙwarewarsa ta haɗa da manyan ayyuka a manyan cibiyoyi masu tasiri irin su New Nigeria Development Company (NNDC) da kuma Hukumar Shirya Jarrabawa ta Yammacin Afirka (WAEC).

Bugu da ƙari, ya kasance ƙwararren mai bada shawara kuma shugaban tsangaya a Makarantar Kasuwanci ta Jos (JBS), makarantar data mayar da hankali wajen bunƙasa harkokin kasuwanci, horas da shugabanni da tsare-tsaren manufofi.

Mista Gomos ya shafe kusan shekaru ashirin yana aiki a Cibiyar Nazarin Siyasa da Dabaru ta Kasa (NIPSS) dake Kuru, inda ya bada gudummawa wajen horar da manyan shugabanni a faɗin Najeriya ta fuskar manufofi, dabaru da ci gaban ƙasa.

Sauran harkokin karatu na sabon Babban Daraktan sun haɗa da digiri na ɗaya dana biyu da ya yi a jami’ar Ahmadu Bello dake Zariya da kuma Jami’ar East Anglia ta kasar Birtaniya.

Har ila yau mamba ne a wasu manyan cibiyoyi na duniya, ciki har da Hubert Humphrey Fellowship (na Jami’ar Minnesota) da Chevening Scholarship na Birtaniya da kuma kasancewarsa mamba a hukumar ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP Fellowship) a Cibiyar Horaswa ta Ƙungiyar Ƙwadago ta Duniya (ILO) a Turin.

Gomos ya halarci manyan horaswar shugabanci a Makarantun Harvard Kennedy, da Jami’ar Chicago Booth School of Business, da Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Durham.

Da yake gabatar da takardar naɗin, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Mista Gomos ya yi amfani da ƙwarewarsa ta fannin jagoranci dabaru, ci gaban cibiyoyi da tsare-tsare don ƙarfafa sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin ta Arewa zuwa wata katafariyar dandalin haɗin gwiwar tsaro da tattalin arziƙin yankin da kuma ci gaba mai ɗorewa a faɗin Arewa.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewan ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa naɗin zai haifar da wani sabon yanayi na zurfafa haɗin gwiwa, da ingantaccen haɗin kai da kuma samar da matakan da suka dace da yankin don fuskantar ƙalubalen Arewa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu
Next Post: Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC

Karin Labarai Masu Alaka

Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.