Ƙungiyar Gwamnonin Arewa ta Najeriya, NNGF, ta bayyana alhininta kan rasuwar dattijo kuma tsohon Gwamnan tsohuwar Jihar Gongola, tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa, Alhaji Bamanga Tukur, tana mai bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi ga Arewa da Najeriya baki ɗaya.
Shugaban NNGF kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ne ya bayyana hakan a cikin saƙon ta’aziyyar da ya fitar a madadin sauran gwamnonin ƙungiyar.
Alhaji Bamanga Tukur ya rasu a Abuja ranar Asabar, 12 ga Satumba, 2026.
Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana marigayin a matsayin ɗaya daga cikin ƙwararrun ma’aikatan gwamnati, ’yan siyasa da masu fafutukar ci gaban tattalin arziƙi da Najeriya ta taɓa samu.
Ya ce hidimar Bamanga Tukur ga Najeriya ta shafe sama da shekaru sittin, inda ya riƙe manyan muƙamai daban-daban da suka haɗa da shugabancin Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya, NPA, Gwamnan tsohuwar Jihar Gongola da kuma Ministan Masana’antu.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yaba da gudunmawar marigayin wajen bunƙasa tattalin arziƙin Afirka, musamman ta hanyar ayyukansa a ƙungiyoyin Africa Business Roundtable da NEPAD Business Group.
Ya ce Bamanga Tukur ya kuma taka muhimmiyar rawa a siyasar Najeriya, musamman a lokacin da ya jagoranci Jam’iyyar PDP a matsayin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa daga shekarar 2012 zuwa 2014.
A cewar Gwamna Inuwa Yahaya, irin ɗimbin ƙwarewar marigayin a harkokin mulki, siyasa, kasuwanci da kuma harkokin Afirka ta sanya shi cikin fitattun mutane na zamaninsa, waɗanda gudunmawarsu za ta ci gaba da kasancewa cikin tarihin Najeriya.
Gwamnan ya ce: “Alhaji Bamanga Tukur ya yi rayuwa mai tsawo mai cike da tasiri, inda ya yi wa Najeriya hidima a muhimman muƙamai daban-daban, tare da bayar da gagarumar gudunmawa wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa, hukumominta da ci gaban siyasa.
“Za a yi matuƙar kewar ɗimbin ƙwarewarsa, hikimarsa da jajircewarsa wajen yi wa al’umma hidima. Rasuwarsa babban rashi ne ga Arewa da Najeriya baki ɗaya.”
Gwamna Inuwa Yahaya ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnati da al’ummar Jihar Adamawa, iyalan marigayin, abokansa da kuma dukkan waɗanda suka san shi tare da yin aiki da shi.
Ya roƙi Allah Ya gafarta wa Alhaji Bamanga Tukur kura-kuransa, Ya saka masa da alheri bisa tsawon shekarun da ya shafe yana yi wa al’umma da ƙasa hidima, sannan Ya ba shi Aljannatul Firdaus.
Rasuwar Bamanga Tukur ta kawo ƙarshen rayuwar wani fitaccen ɗan siyasa da ma’aikacin gwamnati wanda ya shafe sama da shekaru sittin yana taka rawa a harkokin mulki, siyasa da ci gaban tattalin arziƙin Najeriya.

