Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika

Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
Published: September 12, 2026 at 2:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar Alhaji Bamanga Tukur, tsohon Gwamnan farar hula na farko na tsohuwar Jihar Gongola, kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na ƙasa.

Alhaji Bamanga Tukur ya rasu ne a ranar Asabar bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.

A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan, Humwashi Wonosikou, ya fitar a ranar 12 ga Satumba, 2026, Gwamna Fintiri ya bayyana marigayin a matsayin babban ɗan ƙasa, hamshakin ɗan kasuwa kuma fitaccen ɗan siyasa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al’umma hidima.

Gwamna Fintiri ya ce rasuwar Alhaji Bamanga Tukur babban rashi ne ga Jihar Adamawa da Najeriya baki ɗaya, yana mai yaba wa marigayin bisa jajircewarsa, hangen nesa, kishin ƙasa da gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar da ƙasa.

Ya ce shi da kansa zai yi kewar shawarwari masu amfani da hikimar da marigayin ke bayarwa kan al’amuran jihar da ƙasa.

Gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, abokansa, abokan hulɗarsa da al’ummar Jihar Adamawa, yana mai kira gare su da su samu ƙwarin gwiwa daga kyakkyawan tarihin hidima da jagorancin da ya bari.

A matsayin girmamawa ga marigayin da kuma karrama irin gudunmawar da ya bayar, Gwamna Fintiri ya ayyana kwanaki uku na zaman makoki a fadin Jihar Adamawa.

A yayin zaman makokin, za a sauke tutocin gwamnatin jihar zuwa rabin sandar tuta.

Gwamna Fintiri ya kuma roƙi Allah Ya gafarta wa Alhaji Bamanga Tukur kura-kuransa, Ya sa Aljannar Firdausi ce makomarsa, tare da bai wa iyalansa da sauran waɗanda rasuwar ta shafa ƙarfin zuciyar jure wannan babban rashi.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu

Karin Labarai Masu Alaka

Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
CP Chuso Ya Yaba da Matakan Gwamnatin Gombe Wajen Rage Rikicin Makiyaya Da Manoma Afrika
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NDPHC Ta Yi Alkawarin Tallafa Wa Gombe Wajen Inganta Wutar Lantarki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.