Hukumar tsaron gabar tekun Libya ta fara jan wani jirgin ruwa mai ɗauke da iskar gas mai narkewa (LNG) da ya lalace, wanda ƙasashen yankin Bahar Rum da dama suka yi gargadin cewa na iya haifar da haɗarin muhalli, bayan ya yi makonni yana yawo ba tare da matuƙa ba, kamar yadda Gwamnatin Haɗin Kan Ƙasa da ke Tripoli (GNU) ta bayyana.
Jirgin mai ɗauke da tutar Rasha mai suna Arctic Metagaz, wanda ke ɗauke da iskar LNG daga tashar Murmansk ta yankin Arctic, ya kasance yana yawo tun farkon watan Maris, lokacin da Ma’aikatar Sufuri ta Rasha ta ce jiragen ruwa marasa matuƙa na Ukraine sun kai masa hari.
Ba tare da ma’aikata a cikinsa ba, daga ƙarshe jirgin ya kusanto gabar tashar jiragen ruwa ta Zuwara da ke yammacin Libya.
Ƙasashen Italy, France, Spain da wasu ƙasashe shida (6) na kudancin Tarayyar Turai sun aika wasiƙa ga Hukumar Tarayyar Turai a makon da ya gabata, suna gargadin cewa jirgin na haifar da “barazana ta gaggawa kuma mai tsanani ga wani babban bala’in muhalli.”
Ministan Sufuri na gwamnatin GNU, Mohamed Al-Shahoubi, ya ce a cikin wani saƙon bidiyo cewa an ɗora wa Hukumar Mai ta Ƙasa a Libya alhakin sauke kayan da ke cikin jirgin na Rasha. Ya ƙara da cewa ana haɗa kai ta hannun Ma’aikatar Harkokin Waje da hukumomin Rasha da Malta domin ɗaukar matakan tabbatar da tsaron zirga-zirgar ruwa a yankin Bahar Rum.


