Rundunar mayakan Najeriya ta fada ranar laraba cewa, dakarun Amurka da za su iso kasar cikin makon ni masu zuwa ba zasu je fagen daga ba, duk wani al’amari na tsaron kasar yana hanun dakarun Najeriya.
Wannan ya biyo bayan kalaman da wani jami’in Amurka yayi ranar talata cewa ma’aikatar tsaron Amurka da ake kira Pentagon zata tura wata tawagar sojojinta su harasda dakarun Najeriya dabarun yaki da ‘yan bindiga masu ikirarin jihadi, makonni bayanda shugaban Amurka Donald Trump, ya bada umarnim kai farmaki kan mayakan a Najeriya.
A makon jiya ne ma’aikatar tsaron Amurkan ta bada labarin ta tura wata ‘yar karamar tawaga zuwa kasar ba tare da bada wani haske kan lamarin ba, wannan shine karon farko da Amurka ta tabbatar da kasancewar jami’anta a Najeriya.
Kakakin helkwatar tsaro ta Najeriya Sama’ila Uba, ya gayawa kamfanin dilancin labarai na Reuters cewa, hukumomin kasar a Abuja su suka bukaci Washington ta turo da sojojin domin horaswa da shawarwari a wurare daban daban.


