Kamfanin mai na Aramco mallakin gwamnatin Saudiyya na kokarin canza hanyar da yake bi wajen fitar da danyen man fetur zuwa tekun bahar maliya don kaucewa mashigin ruwa na Hormuz a cewar wasu majiyoyi a ranar Talata.

Saudiyya da sauran kasashen yankin tekun fasha masu arzikin man fetur sun kasa wucewa da tankunan man su ta mashigin ruwa na Hormuz tun bayan da Amurka da Isra’il suka kaiwa Iran hari.
An jingine daruruwan jirage a kowanne bangare na mashigin ruwa saboda taka tsantsan. Kamfanin Aramco na Saudiyya na neman ci gaba da fitar da mai yadda ya saba ta sauya hanya zuwa tashar gabar kogin bahar maliya dake Yanbu.


