Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna
Published: January 2, 2026 at 12:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Rasha da Ukraine suna zargin juna da auna hare hare kan farar hula a ranar farko ta sabuwar shekara, inda Rasha tayi zargin Ukraine ta kai mummunar hari akan wai O’tel a yankin kudancin kasar data mamaye, yayin da hukumomi a Kyivi suke zargin Rasha ta auna hare hare kan tashoshin makamashin wutan lantarki.

Rahotannin nan suna zuwa ne a dai dai lokacin da aka zafafa yin shawarwari da zummar kawo karshen yakin na kusan shekaru hudu, ko wacce daga cikin kasashen biyu masu gaba da juna, tana zargin dayar da kokarin cewa ra’ayinta ne ya fi samun karbuwa da goyon bayan shugaban Amurka.

“A ranar sabuwar shekara, da-gangan Rasha ta auna Ukraine da hare hare da jiragen drones da basu da matuka cikin dare.”

Shugaba Volodymyr Zelensky ya rubuta a shafin sa dake dandalin Telegram, yana mai cewa a hare haren, Rasha ta auna tashoshin samar da wutan lantarki a yankunan kasar bakwai.

A nata bangaren Rasha ta zargi Ukraine cewa ta kashe akalla mutane 24 ciki har da jariri a wani hari data kai da jiragen drones kan wani O’tel da wurn cin abinci da shakatawa a yayinda mutane suke murnar shigar sabuwar shekara a yankin Ukraine na Kherson dake kudancin kasar.

Sai dai da take magana, rundunar mayakan Ukraine wacce ta sha sukar Rasha a kan kai hare hare kan farar hula, tace hare haren da take kaiwa duka tana auna su ne kan cibiyoyin soja da kuma tashoshin makamashi, amma bata ce komi ba kan zargin kai hari kan O’tel ba.

Shugaba Zelensky yace, harin na Rasha yayinda ake hutun sabuwar shekara, ya nuna cewa Ukraine ba zata iya jurewa jinkiri kan kayan tsaro ta sararin samaniya ba.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi
Next Post: Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu

Karin Labarai Masu Alaka

An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
  • “Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.