Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta
Published: December 6, 2025 at 5:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya ta sake tabbatar da aniyyarta na kare haƙƙin ’yan jarida da inganta walwalar su, yayin da ta bayyana nasarorin da ta cimma tare da sabbin shirye shiryen da take kaddamarwa a taron shugabannin yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Yola, Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi, ya bayyana wannan kuduri a taron da aka yi a cibiyar NUJ ta Yola, inda ya jaddada bukatar haɗin kai domin farfaɗo da ƙarfinsu na ƙungiya a wannan lokaci da ake yawan samun barazana, tsangwama da cin zarafi ga ’yan jarida a sassa daban daban na ƙasar.

Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi ya bayyana cewa shirin ƙungiyar na inganta walwalar membobin ta ya haɗa da ƙaddamar da inshorar rayuwa da inshorar lafiya ga dukkan ’yan jarida masu aiki, yana mai nuna damuwa da cewa a halin yanzu, ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na ’yan jarida ne ke da inshora.

Yace tsarin inshorar lafiyar zai yi daidai da sabon tsarin ƙasa domin rage nauyin kuɗin magani da suke biya daga aljihun su.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar na ƙoƙarin ganin an inganta albashin ’yan jarida ta hanyar rubutawa da mika kudirin dokar Media Enhancement Bill ga Majalisar Dokoki ta tarayya domin a duba shi tare da amincewa.

Shugaban ya yi kira ga Gwamnan jihar Adamawa da ya tallafa wa ƙungiyar ta hanyar samar da sabuwar Mota kirar bas da kuma sake fasalin sakatariyar NUJ ta jihar domin inganta ayyukan ’yan jarida da jin daɗin su.

Ya kuma bayyana cewa ƙungiyar ta samu nasarar sakin ɗan jarida, Mista Matthew Ojo, wanda aka tsare a Jamhuriyar Benin, ta hanyar haɗin kai da jakadancin kasa da jami’an Najeriya.

Wannan, a cewar sa, wani babban misali ne da ke nuna yadda NUJ ke tsaya wa ’yan jarida, ko da kuwa ba cikakken mamba ba ne.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026,
Next Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.