Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta
Published: December 6, 2025 at 5:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya ta sake tabbatar da aniyyarta na kare haƙƙin ’yan jarida da inganta walwalar su, yayin da ta bayyana nasarorin da ta cimma tare da sabbin shirye shiryen da take kaddamarwa a taron shugabannin yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Yola, Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi, ya bayyana wannan kuduri a taron da aka yi a cibiyar NUJ ta Yola, inda ya jaddada bukatar haɗin kai domin farfaɗo da ƙarfinsu na ƙungiya a wannan lokaci da ake yawan samun barazana, tsangwama da cin zarafi ga ’yan jarida a sassa daban daban na ƙasar.

Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi ya bayyana cewa shirin ƙungiyar na inganta walwalar membobin ta ya haɗa da ƙaddamar da inshorar rayuwa da inshorar lafiya ga dukkan ’yan jarida masu aiki, yana mai nuna damuwa da cewa a halin yanzu, ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na ’yan jarida ne ke da inshora.

Yace tsarin inshorar lafiyar zai yi daidai da sabon tsarin ƙasa domin rage nauyin kuɗin magani da suke biya daga aljihun su.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar na ƙoƙarin ganin an inganta albashin ’yan jarida ta hanyar rubutawa da mika kudirin dokar Media Enhancement Bill ga Majalisar Dokoki ta tarayya domin a duba shi tare da amincewa.

Shugaban ya yi kira ga Gwamnan jihar Adamawa da ya tallafa wa ƙungiyar ta hanyar samar da sabuwar Mota kirar bas da kuma sake fasalin sakatariyar NUJ ta jihar domin inganta ayyukan ’yan jarida da jin daɗin su.

Ya kuma bayyana cewa ƙungiyar ta samu nasarar sakin ɗan jarida, Mista Matthew Ojo, wanda aka tsare a Jamhuriyar Benin, ta hanyar haɗin kai da jakadancin kasa da jami’an Najeriya.

Wannan, a cewar sa, wani babban misali ne da ke nuna yadda NUJ ke tsaya wa ’yan jarida, ko da kuwa ba cikakken mamba ba ne.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026,
Next Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.