Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta
Published: December 6, 2025 at 5:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Ƴan Jarida ta Najeriya ta sake tabbatar da aniyyarta na kare haƙƙin ’yan jarida da inganta walwalar su, yayin da ta bayyana nasarorin da ta cimma tare da sabbin shirye shiryen da take kaddamarwa a taron shugabannin yankin Arewa maso Gabas da aka gudanar a Yola, Jihar Adamawa.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi, ya bayyana wannan kuduri a taron da aka yi a cibiyar NUJ ta Yola, inda ya jaddada bukatar haɗin kai domin farfaɗo da ƙarfinsu na ƙungiya a wannan lokaci da ake yawan samun barazana, tsangwama da cin zarafi ga ’yan jarida a sassa daban daban na ƙasar.

Kwamared Alhassan Yahaya Abdullahi ya bayyana cewa shirin ƙungiyar na inganta walwalar membobin ta ya haɗa da ƙaddamar da inshorar rayuwa da inshorar lafiya ga dukkan ’yan jarida masu aiki, yana mai nuna damuwa da cewa a halin yanzu, ƙasa da kashi ɗaya cikin ɗari na ’yan jarida ne ke da inshora.

Yace tsarin inshorar lafiyar zai yi daidai da sabon tsarin ƙasa domin rage nauyin kuɗin magani da suke biya daga aljihun su.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar na ƙoƙarin ganin an inganta albashin ’yan jarida ta hanyar rubutawa da mika kudirin dokar Media Enhancement Bill ga Majalisar Dokoki ta tarayya domin a duba shi tare da amincewa.

Shugaban ya yi kira ga Gwamnan jihar Adamawa da ya tallafa wa ƙungiyar ta hanyar samar da sabuwar Mota kirar bas da kuma sake fasalin sakatariyar NUJ ta jihar domin inganta ayyukan ’yan jarida da jin daɗin su.

Ya kuma bayyana cewa ƙungiyar ta samu nasarar sakin ɗan jarida, Mista Matthew Ojo, wanda aka tsare a Jamhuriyar Benin, ta hanyar haɗin kai da jakadancin kasa da jami’an Najeriya.

Wannan, a cewar sa, wani babban misali ne da ke nuna yadda NUJ ke tsaya wa ’yan jarida, ko da kuwa ba cikakken mamba ba ne.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026,
Next Post: Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka Labarai
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.