An sanar da nadin Mojtaba Khamenei a matsayin sabon Jagoran Juyin Juya Halin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, jin kadan bayan rasuwar tsohon jagoran ƙasar, Ali Khamenei.

Sabon jagoran ya gaji muƙamin ne a wani lokaci mai cike da ƙalubale a yankin Gabas ta Tsakiya, inda ake fuskantar takaddama mai tsanani tsakanin Iran da wasu ƙasashe, ciki har da Israel.
A cikin sakonsa na farko ga al’umma, Mojtaba Khamenei ya bayyana cewa manufofin ƙasar Iran na ci gaba da shirinta na makamashin Nukiliya da kuma tsayawa tsayin daka wajen kare muradunta a yankin ba za su sauya ba. Ya jaddada cewa Iran za ta ci gaba da bin tafarkin da aka gada daga jagorancin da ya gabata.
Ya kuma yi nuni da cewa ƙasar na cikin shiri da cikakken tsaro, yana mai bayyana Iran a matsayin ƙasa mai ƙarfin guiwa wadda take da isassun dabaru da ƙarfin kare kanta daga duk wata barazana ta waje.
Masu sa ido kan harkokin siyasar duniya na kallon wannan sauyi a matsayin wani sabon babi a tarihin jagorancin Iran, musamman a daidai lokacin da ake fama da rikice-rikice da takaddama a yankin Gabas ta Tsakiya.


