Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
Published: January 14, 2026 at 9:51 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mutane shida sun rasa rayukansu yayin da wata babbar mota dauke da yashi ta kutsa cikin wani coci a yankin Epe na Jihar Lagos da yammacin Litinin.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:30 na dare a titin Hospital Road, lokacin da motar ke gangarowa zuwa zagaye (roundabout) sai birkinta ya lalace, direban ya rasa iko, motar ta kutsa cikin cocin.

Wasu masu ibada sun jikkata, yayin da jami’an agajin gaggawa na jihar Lagos suka isa wurin domin ceto wadanda suka makale.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa direban motar ya tsere bayan hatsarin.

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da mutuwar mutane shida, tare da bayyana cewa motar ba ta da rajista.

An kai gawarwakin wadanda suka mutu dakin ajiye gawa, yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC
Next Post: Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya
Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.