Hukumomin Uganda sun maido da wasu layukan intanet na kasar cikin daren asabar a bayan da aka ayyana cewa shugaba Yoweri Museveni mai shekaru 81 da haihuwa ya lashe wa’adi na 7 a kan mulki, ma’ana zai shafe shekaru 50 da wani abu yana mulkin kasar.

‘Yan adawa dai sun yi watsi da sakamakon zaben da aka bayyana a zaman na bogi.
Da misalin karfe 11 na daren asabar mutanen kasar ta Uganda suka ce sun fara iya hawa kan intanet, inda wasu kamfanonin sadarwa na kasar suka aike da sako ga kwastomominsu cewa hukumomi sun ba su iznin maido da intanet, amma kuma su ci gaba da toshe hanyoyin hawa kan shafukan sada zumunci.
Hukumar sadarwa ta Uganda ta ce ta bada umurnin katse hanyoyin intanet ne domin dakile yada jita-jita da karairayi da yin magudin zabe. Amma ‘yan hamayya sun soki wannan, suna masu fadin cewa an yi hakan ne kawai domin garkame duk wani fanni na zaben domin tabbatar da cewa Museveni ne ya lashe shi.
A ranar asabar, hukumar zabe ta Uganda ta ce Museveni ya lashe zaben rana4 akhamis da kashi 71 cikin 100 yayin da babban abokin hamayyarsa Bobi Wine ya samu kashi 24 cikin 100.


