A ci gaba da shirye-shiryen Gasar Kwallon Kafa ta Masarautun Jihar Gombe, wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Shugaban Gasar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe, ta kai ziyara fadojin sarakuna goma sha biyar a faɗin jihar Gombe.
Da yake bayyana manufar ziyarar, Ahmed Shuaibu Gara Gombe ya ce irin waɗannan wasanni na taimakawa wajen ƙarfafa zumunci, kyautata alaƙa, da kuma ƙulla abota a tsakanin matasan masarautun jihar.
Shugaban Gasar ya bayyana cewa duk ƙungiyar da ta zo mataki na farko za ta lashe kofin gasar tare da naira miliyan biyar, yayin da ta biyu za ta samu naira miliyan uku, sai kuma ta uku wadda za a ba naira miliyan biyu.
Ya ƙara da cewa akwai kuma wasu ƙananan kyaututtuka da za a bai wa ‘yan wasa da ƙungiyoyin da suka yi fice a yayin gasar.
A nasu jawaban, sarakunan jihar sun nuna jin daɗinsu da wannan yunƙuri, tare da jaddada goyon bayansu da haɗin kai domin ganin an gudanar da gasar cikin nasara.


