Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya.
Published: December 4, 2025 at 11:40 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 5, 2025

Kyaftin din Super Eagles William Troost-Ekong ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon kafa na kasa da kasa.

Hakan yasa dan wasan mai shekaru 32 ba zai buga gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe ba, wanda hakan shine ya kasance babban gasa ta farko da Najeriya za ta halarta ba tare da shi ba cikin kusan shekaru 10.

Troost-Ekong, wanda ya yi wasanni 83 kuma ya buga manyan gasa biyar, ya ce wannan shawarar ta zo ne da cikin kwanciyar hankali da sanin cewa a duk wadannan muhimman abubuwan da na yi na bayar da duk wata gudumawa da nake da shi.”

Da yake tunani game da tafiyarsa, ya ce sanya rigar babban kungiyar kwallon kafar Najeriya “ya fi buga kwallon kafa.

Tsohon kyaftin din Super Eagles ya bayyana wasansa na farko a shekarar 2015 a matsayin lokacin da komai ya canza, yana tunawa da yadda marigayi Stephen Keshi ya amince da shi tun da farko “in ji shi.

Troost-Ekong ya nuna jin dadi na damar da ya samu na jagorantar Najeriya, musamman a lokacin gasar AFCON ta 2023, inda aka nada shi Dan wasan Gasar bayan ya zura kwallo a wasan karshe.

“Wannan gasar ta koya min abin da ake nufi da zama dan Najeriya: muna fafatawa cikin wahala kuma muna kokari,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa magoya baya da abokan wasansa wadanda suka tafiya tare ta tsawon shekaru goma.

An haife William a ƙasar Netherlands mahaifiyarsa ‘yar kasar Holland mahaifinsa dan Najeriya, maisuna Troost-Ekong ya wakilci Netherlands a matakin matasa kafin daga bisani ya sadaukar da kansa ga Najeriya.

Ya fara buga wasa a matakin farko a watan Yunin 2015 a wasan share fagen shiga gasar AFCON da Chad.

Kwallaye biyar da ya ci a gasar cin kofin kasashen Afirka sun kasance mafi yawan jimillar kwallaye da wani mai tsaron baya ya ci a tarihin gasar.

Troost-Ekong ya buga wasanin kwallon kafa a kasashen Turai, inda ya yi wasa a Ingila, Italiya, Turkiyya da Girka kafin ya koma PAOK a watan Yulin 2023.

A watan Agustan 2024, ya koma ƙungiyar Al-Kholood ta Saudiyya.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel
Next Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025 Wasanni
Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Yace Yana Nan Daram a Jam’iyar PDP Siyasa
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.