Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16
Published: December 17, 2025 at 8:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani bayahude dan kama-wuri-zauna ya bindige wani Bafalatsine mai shekara 16 da haihuwa har lahira ranar talata a wani gari mai suna Tuqu dake yankin yammacin kogin Jordan, jim kadan a bayan da aka yi jana’izar wani matashin.

Yahudawa ‘yan kama wuri zauna sun kara yawan hare-haren da suke kaiwa kan Falasdinawa a yankin yammacin kogin Jordan tun bayan barkewar yaki a kan gaza, inda MDD ta fada cikin wani rahoto irin wadannan hare-hare sun yi muni zuwa adadin da ba a taba gani ba a watan oktoba.

Magajin garin na Tuqu, Mohammed al-Badan, ya fada ta wayar tarho cewa a bayan da aka yi jana’izar Ammar Sabah mai shekaru 16 wanda sojojin Isra’ila suka kashe, wani bayahude dan kama wuri zauna ya harbi wani matashin, shi ma mai shekara 16 da haihuwa, Muheeb Jibril, a kai, ya kuma kashe shi.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta ce sojojin Isra’ila sun kashe Sabah lokacin da suka kai farmaki ranar litinin a garin.

Akwai Falasdinawa kimanin miliyan biyu da dubu 700 dake zaune a yankin yammacin Kogin Jordan karkashin mamayar sojojin Isra’ila.

Isra’ila ta giggina garuruwa da unguwanni ma yahudawa a yankunan Falasdfinawan da ta kwace karfi da yaji sai dai akasarin kasashen duniya suna daukar wadannan matsugunan yahudawa a zaman na haramun, kuma akwai kudurori da yawa na Kwamitin Sulhun MDD da suka nemi Isra’ila da ta daina kakkaba irin wadannan garuruwan a yankunan na falasdinawa.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka
Next Post: Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Jakadan Kasar Sin a Najeriya Ya Ziyarci Tinubu Najeriya
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
  • Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.