Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada
Published: December 3, 2025 at 8:42 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 4, 2025

‘Yan majalisun dokokin tarayya a nan Amurka su na kara zafafa neman binciken sakataren tsaro Pete Hegseth, dangane da wani lamari na bude wuta a karo na biyu a kan wani jirgin ruwan da aka kai ma farmaki daga farko, matakin da idan ya tabbata zai zamo abinda ya karya dokar yaki da kuma dokokin Amurka.

Sanata Roger Wicker, dan jam’iyyar Republican daga Jihar Mississippi, kuma shugaban kwamitin kula da harkokin soja na majalisar dattijai, yace wannan zargi ne mai karfi, kuma shine dalilin da ya sa tilas su gudanar da bincike.

Jiya talata, Hegseth ya kare hari na biyu da aka kai kan wannan jirgin ruwa, yana mai cewa rashin kyawun yanayi a lokacin kai harin na farko shi ya janyo hakan, yana mai cewa wuta da hayaki sun tashi a lokacin harin na farko kuma shi bai ga wani wanda ya tsira da rai ba a lokacin da aka bada umurnin sake bude wuta a kan jirgin ruwan.

Amma ana samun karin ‘yan majalisar dokoki daga dukkan jam’iyyu biyu da kuma kwararru kan harkokin soja dake fadin cewa harin na ranar 2 ga watan Satumba, matakin soja ne na haramun.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu
Next Post: Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5 Labarai
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.