Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel Afrika
  • Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki Afrika
  • Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba Afrika

Zulum Ya Jinjinawa Hadiza Aliyu Kan Naɗin Ta A Matsayin Babbar Editar NAN
Published: August 30, 2026 at 9:56 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Borno a Arewa Maso Gabashin Najeriya Farfesa Babagana Umara Zulum, ya taya Hajiya Hadiza Mohammed Aliyu murnar naɗin da aka yi mata a matsayin mace ta farko da ta zama Babbar Edita (Editor-in-Chief) ta Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN).

Hadiza Aliyu, wadda ’yar asalin Jihar Borno ce, ita ce mace ta farko da za ta jagoranci sashen edita na NAN tun bayan kafuwar kamfanin sama da shekaru 40 da suka gabata.

Ta yi karatun Sadarwa da Harkokin Yaɗa Labarai (Mass Communication) a Jami’ar Maiduguri.

A cikin wata sanarwa da Mai Ba Gwamna Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Dauda Iliya, ya fitar, Gwamna Zulum ya bayyana Hadiza Aliyu a matsayin ƙwararriyar editan labarai, mai ladabi, jajircewa da ƙwarewa, wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aiki a NAN.

Gwamna Zulum ya ce a madadin gwamnatin da al’ummar Jihar Borno, yana taya Hadiza Mohammed Aliyu murnar wannan babban matsayi da ta samu.

Ya bayyana jin daɗinsa da labarin naɗin nata, musamman kasancewarta shugabar tawagar editoci da ’yan jaridu sama da 500 da ke aiki a ofisoshin NAN daban-daban a faɗin ƙasar da kuma yankuna 18.

Gwamnan ya kuma buƙaci sabuwar Babbar Editar ta ci gaba da kare ƙa’idojin aikin jarida da suka sanya NAN ta zama amintacciyar kafar samun labarai.

Ya ƙara jaddada mata muhimmancin ci gaba da yaƙi da labaran ƙarya, bayanan yaudara, yaɗa bayanan ƙarya da kalaman ƙiyayya, musamman yayin da ƙasar ke tunkarar lokacin yakin neman zaɓe.

Gwamna Zulum ya yi mata fatan samun nasara a wa’adinta na mulki, tare da fatan za ta jagoranci harkokin kamfanin yadda ya kamata.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Yamai Cikin Rashin Tabbas Bayan Karar Harbe-Harbe Da Aka Ji
Next Post: Manoma Da Makiyaya: An Bukaci A Gaggauta Tantance Hanyoyin Shanu Da Iyakoki A Dukku

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
‘Yan Sandan Gombe Sun Yi Taron Gaggawa Da Jam’iyyun Siyasa Da INEC Kan Tsaro Labarai
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato Afrika
CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel
  • Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki
  • Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe
  • ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
  • Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Zata Kara Samar Da Makamai Amurka
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.