Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin Afrika
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala Afrika
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida Afrika
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana Afrika
  • GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe Afrika

Cutar Mashako: Gwamnatin Gombe Ta Fara Rigakafin Gaggawa A Makarantu
Published: September 20, 2026 at 3:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe ta fara wani shirin rigakafin cutar diphtheria na gaggawa, bayan da aka samu rahoton mutane kusan 332 da suka kamu da cutar a ƙananan hukumomi huɗu na jihar.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Akko, Gombe, Kwami da Funakaye.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Gombe ta umarci shugabannin makarantu a faɗin jihar da su ba jami’an lafiya cikakken haɗin kai yayin gudanar da aikin rigakafin.

A cewar umarnin ma’aikatar, kashi na farko na aikin rigakafin zai gudana daga ranar 20 zuwa 24 ga watan Satumba na shekarar 2026.

Ma’aikatar ta bayyana cewa za a yi wa yara kashi na biyu na rigakafin kwanaki 14 bayan an yi na farko, yayin da za a gudanar da kashi na uku kuma na ƙarshe bayan kwanaki bakwai.

An kuma umarci shugabannin makarantu da su wayar da kan ɗalibai, iyaye, ƙungiyoyin iyaye da malamai (PTA), da kwamitocin kula da makarantu (SBMC) game da muhimmancin aikin rigakafin.

Haka kuma, an buƙaci makarantu su bai wa jami’an lafiya da aka amince da su damar shiga wajen ɗalibai domin gudanar da rigakafin.

Ma’aikatar ta kuma yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su tallafa wa matakan da ake ɗauka domin dakile yaɗuwar cutar a jihar.

Cutar diphtheria cuta ce mai saurin yaɗuwa wadda kwayar cuta ke haifarwa, kuma galibi tana shafar hanyoyin numfashi na sama. Ana iya yaɗa ta ta hanyar ɗigon ruwa daga numfashin mutum mai ɗauke da cutar ko kuma ta hanyar kusanci da wanda ya kamu da ita.

Barkewar cutar ta sa hukumomi ƙara kaimi wajen gudanar da rigakafi da wayar da kan jama’a, musamman a makarantu da al’ummomin da ke cikin ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

Hukumomin lafiya na ci gaba da kira ga jama’a da su ba jami’an rigakafi haɗin kai domin taimakawa wajen dakile yaɗuwar cutar da kare lafiyar al’umma.

Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin

Karin Labarai Masu Alaka

China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Cutar Mashako: Gwamnatin Gombe Ta Fara Rigakafin Gaggawa A Makarantu
  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala
  • Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
  • Farashin Mai Ya Ragu A Kasuwar Duniya Amurka
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.