Masu kaɗa ƙuri’a sun fito da yawa a rumfunan zaɓe daban-daban a cikin birnin Gombe domin zaɓen sabon wakilin mazabar tarayya ta Gombe–Kwami–Funakaye, yayin da zaɓen cike gurbi ke gudana cikin lumana.
An fara gudanar da aikin da misalin ƙarfe 8:30 na safiyar yau, inda aka ga masu kaɗa ƙuri’a, ciki har da masu buƙata ta musamman, suna gudanar da tantancewa tare da kaɗa ƙuri’unsu ga ’yan takarar da suka zaɓa.
Haka kuma, an samu irin wannan yanayi a Makarantar Firamare ta Bubayero da wasu rumfunan zaɓe a sassan birnin Gombe, inda jama’a suka fito domin gudanar da haƙƙinsu na zaɓe.
Wasu daga cikin masu kaɗa ƙuri’ar da suka yi magana bayan sun kada ƙuri’a sun bayyana gamsuwarsu da yadda ake gudanar da zaɓen, inda suka ce sun zaɓi ’yan takarar da suke ganin za su iya wakiltar muradunsu da kuma magance matsalolin da al’ummominsu ke fuskanta.
A Makarantar Firamare ta Hassan Central, Kwamishinan Ƙasa na INEC mai kula da shiyyar Arewa maso Gabas, Rear Admiral Jamila Abubakar Malafa, mai ritaya, ta sa ido kan yadda ake gudanar da zaɓen.
Rear Admiral Malafa ta bayyana zaɓen a matsayin wanda ke gudana cikin lumana, tare da yaba wa jami’an zaɓe bisa yadda suke gudanar da ayyukansu.
Ta kuma bayyana kwarin gwiwa cewa za a kammala aikin zaɓen cikin lumana.
Rear Admiral Malafa ta ƙara da cewa dokar zaɓe ta yanzu ta bai wa masu kaɗa ƙuri’a damar sabunta bayanansu a kusa da wuraren da suke, abin da ta ce yana taimakawa wajen sauƙaƙa tsarin zaɓe ga masu kaɗa ƙuri’a.
A nasa bangaren, Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ci Gaban Ƙananan Hukumomi ta Gombe ta Kudu, Alhaji Dalha Adamu Boderi, ya yaba da yawan fitowar masu kaɗa ƙuri’a.
Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa kan sakamakon zaɓen.
Kujerar wakilcin mazabar tarayya ta Gombe–Kwami–Funakaye ya samu gibi ne bayan rasuwar tsohon wakilinta, Yaya Bauchi Tongo.
Tongo ya rasu yana da shekaru 62 a wani asibiti da ke Abuja bayan gajeriyar rashin lafiya a ranar Juma’a, 12 ga watan Yunin 2026, lamarin da ya kai ga shirya wannan zaɓen cike gurbi.
Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kira ga ’yan takara da masu kaɗa ƙuri’a da su kiyaye dokokin ƙasa tare da tabbatar da zaman lafiya a duk tsawon lokacin zaɓen.
Gwamnan ya yi wannan kiran ne jim kaɗan bayan ya kada ƙuri’arsa a rumfar zaɓensa da ke Government Science Senior Secondary School, Jekadafari, da misalin ƙarfe 11:06 na safe.
Gwamna Inuwa ya bayyana gamsuwarsa da yawan fitowar masu kaɗa ƙuri’a, duk da cewa zaɓen na cike gurbi ne.
Ya ce rahotannin da ke zuwa masa daga wasu sassan mazabar sun nuna cewa akwai gagarumar goyon baya ga jam’iyyar APC, tare da bayyana kwarin gwiwarsa kan damar da jam’iyyar ke da ita a zaɓen.
Sai dai ya bayyana wannan ne a matsayin ra’ayinsa, inda ya ce nasarar APC a zaɓen za ta kasance wata alama ce da ke nuna irin matsayin jam’iyyar gabanin babban zaɓen 2027.
Shi ma ɗan takarar kujerar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar APC, Dr Jamilu Isiyaku Gwamna, ya kada ƙuri’arsa a rumfar Saidu Mangu 007, da ke Jekadafari Ward.
Bayan kada ƙuri’arsa, Dr Gwamna ya yaba wa jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, kan yadda suka gudanar da zaɓen.
Ya kuma bayyana fatan cewa za a gudanar da babban zaɓen 2027 cikin ingantaccen tsari, tare da ƙara inganta yadda ake gudanar da harkokin zaɓe.


