Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe ta ce ta tura isassun jami’ai da kayan aikin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilan Tarayya ta Gombe-Kwami-Funakaye da za a gudanar ranar Asabar, 19 ga Satumba, 2026.
Rundunar ta ce an shirya matakan tsaron ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro da ke ƙarƙashin Kwamitin Tuntuɓar Hukumomin Tsaro Kan Zaɓe, ICCES.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya bayar da umarnin tura jami’ai da kayan aikin tsaro zuwa ofisoshin INEC, cibiyoyin tattara ƙuri’u, rumfunan zaɓe da sauran muhimman wurare a ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye.
Rundunar ta ce za a takaita zirga-zirga tare da rufe harkokin kasuwanci a ƙananan hukumomin uku daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na yamma ranar zaɓe, sai dai ayyukan da suka shafi muhimman hidimomin jama’a.
Ta kuma bayyana cewa ma’aikatan da ke gudanar da muhimman ayyuka ba za su yi amfani da ƙahon mota na musamman ba, motoci marasa rajista ko motocin da aka rufe lambobin rajistarsu.
Rundunar ta ƙara da cewa jami’an hukumomin tsaro da aka amince da su ƙarƙashin ICCES ne kawai za su samar da tsaro a lokacin zaɓen. Ta ce ba za a ba ƙungiyoyin tsaro na jiha, ƙungiyoyin tsaro masu zaman kansu, jami’an tsaro na kamfanoni ko ƙungiyoyin sa-kai damar gudanar da aikin tsaro a zaɓen ba.
’Yan sanda sun kuma yi gargaɗi kan yaɗa labaran ƙarya, daba, tashin hankali, ɗaukar makamai ko wasu abubuwan da ka iya haddasa rashin zaman lafiya a rumfunan zaɓe.
Rundunar ta buƙaci iyaye da masu kula da matasa da su gargaɗi ’ya’yansu da kada su bari a yi amfani da su wajen tayar da hankali ko aikata laifuka a lokacin zaɓen.
Ta ce duk wanda aka kama yana aikata wani abu da ka iya kawo cikas ga gudanar da zaɓen cikin lumana, za a kama shi kuma a gurfanar da shi gaban kotu.
Rundunar ta buƙaci al’ummar Gombe da su ba jami’an tsaro haɗin kai tare da kai rahoton duk wani abin da suke zargi zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa ko kuma ta lambobin gaggawa 0815 056 7771 da 0903 643 5359.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ne ya sanya hannu kan sanarwar a madadin Kwamishinan ’Yan Sandan jihar Gombe.


