Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin Afrika
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala Afrika
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida Afrika
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana Afrika
  • GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe Afrika

Zaɓen Gombe-Kwami-Funakaye: INEC Ta Buƙaci Masu Zaɓe Da Jami’ai Su Bi Dokoki
Published: September 18, 2026 at 1:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: September 18, 2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta a Najeriya wato INEC, ta raba kayan zaɓe masu muhimmanci da za a yi amfani da su a zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilan Tarayya ta Gombe-Kwami-Funakaye.

An raba kayan zaɓen zuwa ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro.

An gudanar da rabon kayan ne a harabar ofishin Babban Bankin Najeriya, CBN, da ke birnin Gombe.

Jami’in Zaben INEC na Jihar Gombe, Umar Mukhtar Gajiram, ne ya sanya hannu kan kayan zaɓen kafin a raba su, inda ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da aikin.

Gajiram ya bayyana cewa duk wata takardar zaɓe da ba ta ɗauke da sa hannun jami’in da aka tanada ba za a ɗauke ta a matsayin mara inganci.

Ya kuma bayyana cewa za a gudanar da zaɓen a rumfunan zaɓe 903 da ke cikin mazabu 31 a ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye.

Jami’in Zaben ya buƙaci masu kaɗa ƙuri’a da su kasance cikin lumana tare da guje wa duk wani abu da ka iya kawo cikas ga zaman lafiya kafin, lokacin da kuma bayan kammala zaɓen.

Haka kuma, ya yi kira ga jami’an zaɓe da su tabbatar da bin ƙa’idoji da ɗabi’un da hukumar INEC ta tanada domin gudanar da zaɓen cikin gaskiya da adalci.

An sanya hannu kan kayan zaɓen ne a gaban jami’an tsaro, jami’an INEC, wakilan jam’iyyun siyasa da kuma wakilan ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye.

Zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilan Tarayya ta Gombe-Kwami-Funakaye dai zai gudana ne ranar Asabar, 19 ga Satumba, 2026.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe
Next Post: Zaɓen Gombe: ’Yan Sanda Sun Sanar Da Tsauraran Matakan Tsaro Ranar Asabar

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NUJ Ta Kai Ziyarar Jaje GMC Bayan Gobara Ta Lalata Ginin Sashen Talabijin
  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala
  • Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.