Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Gombe, Gombe State Electricity Regulatory Commission (GOSERC), ta gudanar da taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin wayar da kansu kan hurumin hukumar, manufofinta da kuma nauyin da aka dora mata.
Taron da aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Gombe, ya samu halartar wakilan kungiyoyi daban-daban, ciki har da Ƙungiyar Masu Nika Gyada, Ƙungiyar Masu Samar da Ruwan Sha a Roba, COREN, ASUU, sarakunan gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki.
Da yake buɗe taron, Kwamishinan Ma’aikatar Makamashi da Albarkatun Ƙasa na jihar Gombe, Alhaji Sanusi Ahmad Maidalan Pindiga, ya bayyana taron a matsayin wani muhimmin mataki a ƙoƙarin jihar na samun ’yancin kai a fannin makamashi, bunƙasa masana’antu da haɓaka tattalin arziƙi.
Kwamishinan ya ce kafa GOSERC ya samu ne bisa tanadin doka da kundin tsarin mulki da kuma Dokar Wutar Lantarki ta 2023, wadda ta bai wa jihohi damar taka muhimmiyar rawa wajen tsara da kuma kula da kasuwannin wutar lantarki a jihohinsu.
Ya ce Gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ɗauki matakin kafa GOSERC domin rarraba ikon kula da harkokin wutar lantarki, tare da bai wa Jihar Gombe damar kula da tsarin kasuwar wutar lantarki a cikinta.
Tun da farko, Shugaban GOSERC, Alhaji Abba Arabi, ya ce an shirya taron ne domin cimma manufofin da aka kafa hukumar a kansu.
Ya bayyana cewa taron ya kasance wata dama ta sanar da masu ruwa da tsaki game da hurumin hukumar, tare da ba su damar bayar da shawarwari kan yadda za a samar da ingantaccen tsarin kula da wutar lantarki a jihar.
Kwamishiniyar Kula da Harkokin Shari’a ta hukumar, Barrister Talatu Abubakar, ta tabbatar wa mahalarta taron cewa za a duba tare da tantance dukkan shawarwari da ra’ayoyin da ƙungiyoyin da suka halarci taron suka gabatar, domin la’akari da yiwuwar aiwatar da su.
Shi ma wakilin Babban Hakimin Gombe, Alhaji Sammani Babba, ya bayyana kafa GOSERC a matsayin wani muhimmin ci gaba a tarihin bunƙasa Jihar Gombe.
Wakilan Ƙungiyar Masu Nika Gyada, Ƙungiyar Masu Samar da Ruwan Sha a Roba, ASUU da COREN sun bayyana goyon bayansu ga hukumar tare da alkawarin ba ta haɗin kai wajen cimma manufofinta.
Mataimakin Shugaban hukumar, Injiniya Suleman Usman, da Kwamishinan Harkokin Fasaha, Abubakar Sa’ad, sun kuma yi wa mahalarta bayani kan ayyukan hukumar, ciki har da dangantakarta da kamfanonin rarraba wutar lantarki da kuma masu amfani da wutar.
A yayin taron, mahalarta sun gabatar da tambayoyi da shawarwari musamman kan samar da wutar lantarki, tsarin kula da ita, matsalolin masu amfani da wutar da kuma ayyukan Kamfanin Savannah Electricity Company.
Hukumar ta amsa tambayoyin da aka gabatar tare da tabbatar da aniyarta ta samar da ingantaccen, sahihi kuma mai gaskiya tsarin kula da wutar lantarki wanda zai kuma kare muradun masu amfani da wutar lantarki a jihar Gombe.


